Gwamnatin jihar Kebbi ƙarƙashin jagorancin Gwamna Nasir Idris ta rattaba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna (MoU) da kamfanin Kaduna Electricity Distribution Company domin inganta samar da wutar lantarki a faɗin jihar.
Sakataren Gwamnatin jihar, Yakubu Bala Tafida ne ya bayyana hakan yayin da yake cikin tawagar gwamnatin jihar da ke halartar wani muhimmin taron makamashi da ke gudana a birnin London na ƙasar Birtaniya.
A cewarsa, yarjejeniyar na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar na ganin an samu ingantacciyar wutar lantarki ga al’ummar Kebbi, wanda ake sa ran zai ƙarfafa harkokin tattalin arziki, jawo zuba jari, tare da inganta rayuwar jama’a.
Gwamnan ya halarci taron tare da wasu takwarorinsa da suka haɗa da Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal da Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, inda suka tattauna kan hanyoyin bunƙasa zuba jari a fannin makamashi da ci gaban yankuna.
Taron ya haɗa manyan jami’an gwamnati, ƙwararru a fannin makamashi da masu ruwa da tsaki domin lalubo hanyoyin inganta rarraba wutar lantarki a yankin da KEDCO ke aiki.
Gwamnatin Kebbi ta bayyana yarjejeniyar a matsayin wani muhimmin mataki na inganta ababen more rayuwa da samar da yanayi mai kyau ga ci gaba, daidai da tanade-tanaden dokar lantarki ta shekarar 2023 da ke ƙarfafa shigar kamfanoni masu zaman kansu a fannin.
Gwamnatin ta kuma jaddada aniyarta na ci gaba da aiwatar da manufofi da shirye shiryen da za su amfani al’umma, inda wannan haɗin gwiwa a fannin lantarki ke daga cikin muhimman matakan da take ɗauka.


