Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan
Published: April 2, 2026 at 2:28 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: April 2, 2026

Gwamnatin jihar Kebbi ƙarƙashin jagorancin Gwamna Nasir Idris ta rattaba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna (MoU) da kamfanin Kaduna Electricity Distribution Company domin inganta samar da wutar lantarki a faɗin jihar.

Sakataren Gwamnatin jihar, Yakubu Bala Tafida ne ya bayyana hakan yayin da yake cikin tawagar gwamnatin jihar da ke halartar wani muhimmin taron makamashi da ke gudana a birnin London na ƙasar Birtaniya.

A cewarsa, yarjejeniyar na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar na ganin an samu ingantacciyar wutar lantarki ga al’ummar Kebbi, wanda ake sa ran zai ƙarfafa harkokin tattalin arziki, jawo zuba jari, tare da inganta rayuwar jama’a.

Gwamnan ya halarci taron tare da wasu takwarorinsa da suka haɗa da Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal da Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, inda suka tattauna kan hanyoyin bunƙasa zuba jari a fannin makamashi da ci gaban yankuna.

Taron ya haɗa manyan jami’an gwamnati, ƙwararru a fannin makamashi da masu ruwa da tsaki domin lalubo hanyoyin inganta rarraba wutar lantarki a yankin da KEDCO ke aiki.

Gwamnatin Kebbi ta bayyana yarjejeniyar a matsayin wani muhimmin mataki na inganta ababen more rayuwa da samar da yanayi mai kyau ga ci gaba, daidai da tanade-tanaden dokar lantarki ta shekarar 2023 da ke ƙarfafa shigar kamfanoni masu zaman kansu a fannin.

Gwamnatin ta kuma jaddada aniyarta na ci gaba da aiwatar da manufofi da shirye shiryen da za su amfani al’umma, inda wannan haɗin gwiwa a fannin lantarki ke daga cikin muhimman matakan da take ɗauka.

Afrika, Labarai, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos
Next Post: Shugaba Trump Yace Babu Maganar Kawo Karshen Yakin Amurka Da Iran

Karin Labarai Masu Alaka

Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
Hukumar DSS Ta Sake Kama Abubakar Malami Labarai
Harin Ukraine Yayi Mummunan Barna A Rasha Afrika
Rundunar Sojin Amurka Sunfara Ficewa Daga Kasar Sham Amurka
Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika
NITDA Da GOSIDEC Sun Horar Da Ma’aikatan Gombe Don Inganta Ayyukan Gwamnati Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Najeriya Zata Kara Mai Da Take Hakowa Afrika
  • Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri Najeriya
  • Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
  • Ana Sa Ran FIFA Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Najeriya Ta Shigar Kan DR Congo Wasanni
  • Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika
  • Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba Afrika
  • Dakarun Zaman Lafiya Na Majalisar Dinkin Duniya Sun Rasa Rayukan Su Afrika
  • Jami’an Tsaron Pakistan Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.