Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan
Published: April 2, 2026 at 2:28 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: April 2, 2026

Gwamnatin jihar Kebbi ƙarƙashin jagorancin Gwamna Nasir Idris ta rattaba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna (MoU) da kamfanin Kaduna Electricity Distribution Company domin inganta samar da wutar lantarki a faɗin jihar.

Sakataren Gwamnatin jihar, Yakubu Bala Tafida ne ya bayyana hakan yayin da yake cikin tawagar gwamnatin jihar da ke halartar wani muhimmin taron makamashi da ke gudana a birnin London na ƙasar Birtaniya.

A cewarsa, yarjejeniyar na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar na ganin an samu ingantacciyar wutar lantarki ga al’ummar Kebbi, wanda ake sa ran zai ƙarfafa harkokin tattalin arziki, jawo zuba jari, tare da inganta rayuwar jama’a.

Gwamnan ya halarci taron tare da wasu takwarorinsa da suka haɗa da Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal da Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, inda suka tattauna kan hanyoyin bunƙasa zuba jari a fannin makamashi da ci gaban yankuna.

Taron ya haɗa manyan jami’an gwamnati, ƙwararru a fannin makamashi da masu ruwa da tsaki domin lalubo hanyoyin inganta rarraba wutar lantarki a yankin da KEDCO ke aiki.

Gwamnatin Kebbi ta bayyana yarjejeniyar a matsayin wani muhimmin mataki na inganta ababen more rayuwa da samar da yanayi mai kyau ga ci gaba, daidai da tanade-tanaden dokar lantarki ta shekarar 2023 da ke ƙarfafa shigar kamfanoni masu zaman kansu a fannin.

Gwamnatin ta kuma jaddada aniyarta na ci gaba da aiwatar da manufofi da shirye shiryen da za su amfani al’umma, inda wannan haɗin gwiwa a fannin lantarki ke daga cikin muhimman matakan da take ɗauka.

Afrika, Labarai, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos
Next Post: Shugaba Trump Yace Babu Maganar Kawo Karshen Yakin Amurka Da Iran

Karin Labarai Masu Alaka

Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai
Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba Afrika
Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya Labarai
Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada Afrika
Farashin Mai Ya Doshi Dala 100 Kowacce Ganga Afrika
Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Farashin Danyen Mai Ya Fadi A Kasuwar Duniya Afrika
  • Amurkawa Suna Turuwa Zuwa Kasar Faransa Duk Da Rashin Jituwa A Tsakanin Kasashen Amurka
  • Shugaba Trump Ya Bukaci Kasar Iran Ta Mika Wuya Amurka
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
  • Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC Labarai
  • Pakistan Zata Karbi Bakwancin Saudiya, Turkiyya Da Masar Afrika
  • Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya
  • Anyi Rashin Mutane Da Yawa Yayinda Bom Ya Fashe Ana Sallar Magariba Maiduguri Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.