Gwamnatin jihar Gombe, tare da haɗin gwiwar Kamfanin Rift Oil Petroleum Company Limited da ke Abuja, ta ƙaddamar da wani shirin horaswa na musamman ga matasa da masu sana’o’i sama da 100 daga ƙananan hukumomi 11 na jihar, domin inganta ƙwarewarsu da shirya su don cin gajiyar damar aiki a fannin mai da iskar gas.

An fara gudanar da shirin ne a Kwalejin Fasaha ta Gwamnati da Emerald Hotel da ke Gombe, yayin da jihar ke ci gaba da shirye-shiryen farfaɗo da ayyukan bincike da haƙar mai a yankin Kolmani.
Da yake ƙaddamar da shirin, Babban Sakataren Ma’aikatar Makamashi da Albarkatun Ma’adanai ta jihar, Alhaji Suleiman Musa Kwami, ya bayyana cewa manufar horaswar ita ce samar da ƙwararrun ma’aikata na cikin gida da za su iya taka rawa a ci gaban masana’antar mai da iskar gas da ake sa ran za ta bunƙasa a jihar.
Ya ce ma’aikatar ta karɓi buƙatun shiga shirin sama da 400 daga matasa masu sha’awar cin gajiyar damar da fannin zai samar, yana mai yabawa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya bisa goyon bayan da gwamnatinsa ke bayarwa wajen bunƙasa albarkatun makamashi da haɓaka ƙwarewar matasa.
A nasa jawabin, Daraktan Kimiyya, Fasaha da Ilimin Sana’o’i na Ma’aikatar Ilimi ta jihar, Aminu Shehu, ya ce shirin ya yi daidai da manufofin gwamnatin jihar na ƙarfafa matasa ta hanyar koyar da sana’o’i da dabarun zamani da za su taimaka musu samun ayyukan yi.

Shi kuwa mai ba da shawara ga Kamfanin Rift Oil Petroleum Company Limited, Mista Samson Mato, ya buƙaci mahalarta shirin da su mayar da hankali wajen cin moriyar horon, yana mai cewa ƙwarewar da za su samu za ta ƙara musu damar samun aiki a masana’antar mai da iskar gas a faɗin ƙasar nan.
Hakazalika, Ahmad Ardo Muhammad ya jaddada muhimmancin shirin wajen samar da ƙwararrun ma’aikata da za su taimaka wajen bunƙasa tattalin arzikin jihar da ma ƙasa baki ɗaya.
Da yake nasa jawabin, Shugaban Kamfanin Rift Oil Petroleum Company Limited kuma Babban Jami’in Gudanarwa, Injiniya Rabiu Suleiman, ya ce an tsara shirin ne domin wayar da kan al’umma game da muhimmancin masana’antar mai da iskar gas a matsayin wata muhimmiyar hanyar samar da kuɗaɗen shiga da haɓaka tattalin arziki.
Ya kuma yabawa gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya saboda matakan da take ɗauka na tabbatar da cewa Gombe ta amfana da albarkatun mai da ke yankin Kolmani tare da shiga sahun jihohin da ke samar da mai a Najeriya.
Shirin horaswar zai mayar da hankali ne kan fannoni da suka haɗa da girke-girken lantarki da kula da shi, walda da ƙera kayayyaki, aikin kafinta, aikin famfo da sauran sana’o’in fasaha masu alaƙa da harkar mai da iskar gas.


