Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika
  • Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
  • Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika
  • Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika

Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila
Published: December 23, 2025 at 9:26 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, ya amince da korar Adamu Abdullahi Danko da wasu mataimaka uku nan take bayan binciken cin zarafin da aka yiwa, Abdulrahman Abubakar Sheriff, Kansila mai wakiltar gundumar Shamaki a karamar hukumar Gombe.

Matakin wadda Sakataren Gwamnatin jihar Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi ya sanar, ya biyo bayan kafa kwamitin bincike na musamman ne kan lamarin.

Sakamakon binciken kwamitin wanda rahotannin hukumomin tsaro suka tabbatar ne ya kai ga matakin da Gwamnan ya ɗauka.

A cewar Sakataren Gwamnatin Jihar, masu taimakawa gwamnan da abin ya shafa sune, Adamu Abdullahi Danko – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan Harkokin Cikin Gida, da Garba Mohammed Mai Rago – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan harkokin Siyasa, da Rabiu Sulaiman Abubakar – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan Kafafen Sada Zumunta na Zamani da kuma Ali Ibrahim Baban Kaya – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan Hulɗa da al’umma.

Gwamna Inuwa Yahaya ya bada umarnin cewa korar ta fara aiki ne nan take.

An kuma umurci duk jami’an da abin ya shafa su miƙa duk kadarorin gwamnati dake hannunsu ga hukumomin da suka dace ba tare da wani ɓata lokaci ba.

Gwamna Inuwa Yahaya ya sake jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci tashin hankali, rashin ɗa’a da cin zarafi ba, yana mai cewa ba zai lamunci duk abinda zai iya yin barazana ga zaman lafiyar jama’a ko lalata amincin da gwamnatinsa ke da shi a idon al’ummar jihar ba.

Ya tabbatarwa al’ummar jihar Gombe jajircewar gwamnatinsa wajen tabbatar da bin doka da oda, riƙon amana da kuma zaman lafiya sannan ya ƙara da cewa za a ɗauki matakai masu tsauri don kare zaman lafiya da ɗorewar kwanciyar hankalin da jihar take ta fafutukar ɗabbaƙawa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Sojin Ukraine Sun Janye Daga Gabashin Kasar
Next Post: Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya

Karin Labarai Masu Alaka

Haryanzu Abubakar Malami Da Dansa Suna Hannun Hukumar EFCC Labarai
Allah Ya Yiwa Shahararren Dan Jarida Saleh Shehu Ashaka Rasuwa Labarai
Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC Najeriya
Mayakan ISWAP Sun Kai Farmaki Kan Sojojin Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi
  • Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya
  • Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja
  • Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa Afrika
  • Oliseh, Ya Ba Eric Chelle, Shawara Da Ya Zamo Mai Tsauri AFCON 2025. Wasanni
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Donald Trump Yace Basu Cimma Matsaya Da Benjamin Natanyahu Ba Afrika
  • Sojoji Sunkai Farmaki Gidan Dan Adawa A Kasar Uganda Bobi Wine Afrika
  • Hukumar Zabe Ta Saukaka Gudanar Da Rijistar Katin Zabe A Najeriya Labarai
  • Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.