Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila
Published: December 23, 2025 at 9:26 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, ya amince da korar Adamu Abdullahi Danko da wasu mataimaka uku nan take bayan binciken cin zarafin da aka yiwa, Abdulrahman Abubakar Sheriff, Kansila mai wakiltar gundumar Shamaki a karamar hukumar Gombe.

Matakin wadda Sakataren Gwamnatin jihar Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi ya sanar, ya biyo bayan kafa kwamitin bincike na musamman ne kan lamarin.

Sakamakon binciken kwamitin wanda rahotannin hukumomin tsaro suka tabbatar ne ya kai ga matakin da Gwamnan ya ɗauka.

A cewar Sakataren Gwamnatin Jihar, masu taimakawa gwamnan da abin ya shafa sune, Adamu Abdullahi Danko – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan Harkokin Cikin Gida, da Garba Mohammed Mai Rago – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan harkokin Siyasa, da Rabiu Sulaiman Abubakar – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan Kafafen Sada Zumunta na Zamani da kuma Ali Ibrahim Baban Kaya – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan Hulɗa da al’umma.

Gwamna Inuwa Yahaya ya bada umarnin cewa korar ta fara aiki ne nan take.

An kuma umurci duk jami’an da abin ya shafa su miƙa duk kadarorin gwamnati dake hannunsu ga hukumomin da suka dace ba tare da wani ɓata lokaci ba.

Gwamna Inuwa Yahaya ya sake jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci tashin hankali, rashin ɗa’a da cin zarafi ba, yana mai cewa ba zai lamunci duk abinda zai iya yin barazana ga zaman lafiyar jama’a ko lalata amincin da gwamnatinsa ke da shi a idon al’ummar jihar ba.

Ya tabbatarwa al’ummar jihar Gombe jajircewar gwamnatinsa wajen tabbatar da bin doka da oda, riƙon amana da kuma zaman lafiya sannan ya ƙara da cewa za a ɗauki matakai masu tsauri don kare zaman lafiya da ɗorewar kwanciyar hankalin da jihar take ta fafutukar ɗabbaƙawa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Sojin Ukraine Sun Janye Daga Gabashin Kasar
Next Post: Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya

Karin Labarai Masu Alaka

Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC Afrika
Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida Afrika
  • Kasar Mauritius Zata Rage Amfani Da Makamashi Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
  • Wani Bayahude Ya Harbe Bafalatsine Dan Shekaru 16 Tsaro
  • An Gurfaranar Da Wadanda Ake Zargi Takai Hari Gaban Kotu Najeriya
  • ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
  • Yan Fashi Sun Shiga Gidan Alex Iwobi A Ingila Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.