Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe
Published: March 8, 2026 at 4:00 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ƙungiyar Mata Manoma a Najeriya, wato WOFAN, ƙarƙashin jagorancin Hajiya Salamatu Garba, ta raba buhunan shinkafa dubu biyar ga mata a jihar Gombe domin tallafa musu wajen inganta rayuwar iyalansu, a wani shiri da aka gudanar domin tunawa da Ranar Mata ta Duniya.

Da yake jawabi yayin ƙaddamar da rabon tallafin, Shugaban WOFAN a Jihar Gombe, Usman Rayyanu Dabai, ya bayyana cewa shirin ya shafi mata a wasu daga cikin ƙananan hukumomin jihar da suka haɗa da Gombe, Akko, Yamaltu Deba, Kwami da Dukku.

Ya ce an shirya wannan tallafi ne a wani ɓangare na bikin Ranar Mata ta Duniya, domin ƙarfafa mata da kuma taimaka musu su tallafa wa iyalansu, musamman mazajensu, wajen tafiyar da al’amuran gida.

Rayyanu Dabai ya kuma yi kira ga mata a faɗin Jihar Gombe da su ci gaba da bai wa mazajensu haɗin kai a harkokin gida, domin ƙarfafa zaman lafiya da kyakkyawar rayuwar aure.

A nasu jawaban yayin karɓar tallafin, wasu daga cikin sarakunan gargajiya da suka haɗa da Banban Hakimin Gombe, Alhaji Bappah Ibrahim, Hakimin Bokna, Alhaji Abubakar Usman Deba, da Lamidon Akko, Alhaji Umaru Muhammadu Atiku, sun yaba wa Hajiya Salamatu Garba bisa wannan karamci da ta nuna wa al’ummar Jihar Gombe.

Sarakunan gargajiyar sun kuma buƙaci mata a jihar da su zauna lafiya da mazajensu tare da riƙa ba su goyon baya, domin ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kan iyalai.

An gudanar da bikin ƙaddamar da rabon tallafin ne a Makarantar Firamare ta Orji Estate da ke Gombe, inda wakilan mata daga kowace ƙaramar hukuma da abin ya shafa suka halarta domin karɓar nasu kaso na tallafin.

Afrika, Labarai, Najeriya, Nishadi, Rumbun Hotuna

Post navigation

Previous Post: Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi
Next Post: Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Ta Tura Mutane 386 Gidan Yari Afrika
Kasar Gabon Ta Nemi Tallafin Asusun Bada Lamuni Na IMF Afrika
Shugabannin Kasashen Afirka Ta Tsakiya Sun Kamallah Taron Koli Afrika
Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka Afrika
Kasar Botswana Na Samun Kudaden Shiga Da Lu’ulu’u Labarai
Jam’iyyar APC Ta Rantsar Da Sabbin Shugabanni a Jihar Neja Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki Labarai
  • Amurka Ta Kai ‘Yan Cirani Kamaru Afrika
  • Ko Meye Gaskiyar Rade-Radin Zanga-Zanga A Jos Dake Jihar Filato Labarai
  • Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa Labarai
  • Majalisar Dattawan Amurka Ta Amince Da Wata Doka Amurka
  • Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar Amurka
  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
  • ‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.