Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe
Published: March 8, 2026 at 4:00 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ƙungiyar Mata Manoma a Najeriya, wato WOFAN, ƙarƙashin jagorancin Hajiya Salamatu Garba, ta raba buhunan shinkafa dubu biyar ga mata a jihar Gombe domin tallafa musu wajen inganta rayuwar iyalansu, a wani shiri da aka gudanar domin tunawa da Ranar Mata ta Duniya.

Da yake jawabi yayin ƙaddamar da rabon tallafin, Shugaban WOFAN a Jihar Gombe, Usman Rayyanu Dabai, ya bayyana cewa shirin ya shafi mata a wasu daga cikin ƙananan hukumomin jihar da suka haɗa da Gombe, Akko, Yamaltu Deba, Kwami da Dukku.

Ya ce an shirya wannan tallafi ne a wani ɓangare na bikin Ranar Mata ta Duniya, domin ƙarfafa mata da kuma taimaka musu su tallafa wa iyalansu, musamman mazajensu, wajen tafiyar da al’amuran gida.

Rayyanu Dabai ya kuma yi kira ga mata a faɗin Jihar Gombe da su ci gaba da bai wa mazajensu haɗin kai a harkokin gida, domin ƙarfafa zaman lafiya da kyakkyawar rayuwar aure.

A nasu jawaban yayin karɓar tallafin, wasu daga cikin sarakunan gargajiya da suka haɗa da Banban Hakimin Gombe, Alhaji Bappah Ibrahim, Hakimin Bokna, Alhaji Abubakar Usman Deba, da Lamidon Akko, Alhaji Umaru Muhammadu Atiku, sun yaba wa Hajiya Salamatu Garba bisa wannan karamci da ta nuna wa al’ummar Jihar Gombe.

Sarakunan gargajiyar sun kuma buƙaci mata a jihar da su zauna lafiya da mazajensu tare da riƙa ba su goyon baya, domin ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kan iyalai.

An gudanar da bikin ƙaddamar da rabon tallafin ne a Makarantar Firamare ta Orji Estate da ke Gombe, inda wakilan mata daga kowace ƙaramar hukuma da abin ya shafa suka halarta domin karɓar nasu kaso na tallafin.

Afrika, Labarai, Najeriya, Nishadi, Rumbun Hotuna

Post navigation

Previous Post: Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi
Next Post: Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini

Karin Labarai Masu Alaka

NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
Gwamnatin Tinubu Zata Samar Da Wutan Solar A Jami’ar ADUST Wudil Afrika
Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya Afrika
Jaura Ta Bayyana A Wasu Jihohin Amurka Labarai
‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz
  • Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ambaliyar Ruwa Ya Tilastawa Dubban Jama’a Rasa Muhallensu A Morocco Afrika
  • Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
  • Onana Ba Ya Cikin Tawagar Kamaru (AFCON) Wasanni
  • Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
  • Sojojin Amurka Sun Kutsa Cikin Kasar Iran Labarai
  • Shugaban Koriya Ta Arewa Ya Gabatar Da Gwajin Makami Mai Linzami Afrika
  • An Gudanar Da Idin Karamar Sallah A Birnin Niamey Labarai
  • Dakarun Zaman Lafiya Na Majalisar Dinkin Duniya Sun Rasa Rayukan Su Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.