Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Tura Mutane 386 Gidan Yari
Published: April 11, 2026 at 7:28 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayya ta bayyana samun nasarar daure mutum 386 daga cikin mutum 508 da ake tuhuma da laifukan ta’addanci a wata gagarumar shari’ar bai daya da aka gudanar.

Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Gwamnatin kasar , Lateef Fagbemi (SAN), ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai ranar Juma’a. Ya bayyana cewa, Adadin Wadanda Aka Daure Mutum 386, Wadanda Aka Wanke Mutum biyu (2), Sai Wadanda Aka Sallama Mutum takwas (8).

Sauran Wadanda Ba a Kammala Nasu Ba Mutum 112, za a ci gaba da shari’arsu daga ranar 15 zuwa 18 ga watan Yuni.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa an fara wannan shari’ar ce tun ranar Talata a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja. Wadanda aka samu da laifin an yanke musu hukuncin zaman gidan yari daban-daban, kama daga shekara takwas (8) har zuwa daurin rai-da-rai, dangane da nauyin laifin da kowannensu ya aikata.

Fagbemi ya jaddada cewa wannan hukunci wani sako ne ga masu aikata manyan laifuka cewa Najeriya ba za ta amince da ta’addanci ba. Ya kuma jinjina wa alkalai 10 da suka sadaukar da hutunsu na Ista domin gudanar da wannan shari’a ta musamman.

Domin tabbatar da adalci da gaskiya, kungiyoyi da dama sun halarci zaman kotun a matsayin masu sanya ido, ciki har da Kungiyar Lauyoyi ta Najeriya (NBA), Hukumar Kare Hakkin Dan-adam ta Kasa, Kungiyar Amnesty International, Da Wasu kungiyoyin farar hula.

Wannan shari’ar tana daya daga cikin matakai na tara (Phase 9) da gwamnati ke dauka domin dakile matsalar tsaro da kuma tabbatar da cewa wadanda aka dade ana tsare da su sun fuskanci shari’a domin maido da zaman lafiya a kasar.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu
Next Post: Shugaban Ƙasar Djibouti Ya Sake Lashe Zaben Shugaban Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Kasuwannin Hannun Jari Sun Farfado Afrika
Baba Malam Ya Lallasa Abokan Hamayya Da Kuri’u Sama Da Dubu 236 A Zaben Fidda Gwani Afrika
Kasar India Ta Sayi Iskar Gas Daga Iran Labarai
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda Najeriya
Man Da Matatar Dangote Take Fitarwa Zuwa Kasashen Afirka Ya Karu Afrika
Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
  • An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
  • FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Kasar Ghana Ta Bayyana Fataucin Bayi A Matsayin Babban Laifi Afrika
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • Shugaba Trump Ya Bukaci A Cigaba Da Zanga Zanga A Iran Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.