Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Tura Mutane 386 Gidan Yari
Published: April 11, 2026 at 7:28 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayya ta bayyana samun nasarar daure mutum 386 daga cikin mutum 508 da ake tuhuma da laifukan ta’addanci a wata gagarumar shari’ar bai daya da aka gudanar.

Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Gwamnatin kasar , Lateef Fagbemi (SAN), ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai ranar Juma’a. Ya bayyana cewa, Adadin Wadanda Aka Daure Mutum 386, Wadanda Aka Wanke Mutum biyu (2), Sai Wadanda Aka Sallama Mutum takwas (8).

Sauran Wadanda Ba a Kammala Nasu Ba Mutum 112, za a ci gaba da shari’arsu daga ranar 15 zuwa 18 ga watan Yuni.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa an fara wannan shari’ar ce tun ranar Talata a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja. Wadanda aka samu da laifin an yanke musu hukuncin zaman gidan yari daban-daban, kama daga shekara takwas (8) har zuwa daurin rai-da-rai, dangane da nauyin laifin da kowannensu ya aikata.

Fagbemi ya jaddada cewa wannan hukunci wani sako ne ga masu aikata manyan laifuka cewa Najeriya ba za ta amince da ta’addanci ba. Ya kuma jinjina wa alkalai 10 da suka sadaukar da hutunsu na Ista domin gudanar da wannan shari’a ta musamman.

Domin tabbatar da adalci da gaskiya, kungiyoyi da dama sun halarci zaman kotun a matsayin masu sanya ido, ciki har da Kungiyar Lauyoyi ta Najeriya (NBA), Hukumar Kare Hakkin Dan-adam ta Kasa, Kungiyar Amnesty International, Da Wasu kungiyoyin farar hula.

Wannan shari’ar tana daya daga cikin matakai na tara (Phase 9) da gwamnati ke dauka domin dakile matsalar tsaro da kuma tabbatar da cewa wadanda aka dade ana tsare da su sun fuskanci shari’a domin maido da zaman lafiya a kasar.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu
Next Post: Shugaban Ƙasar Djibouti Ya Sake Lashe Zaben Shugaban Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Gombe Ya Ƙara Tallafin N148.76bn Domin Aiwatar da Sabon Tsarin Albashi A Jami’ar Gombe Afrika
Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya
Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya Afrika
Iran Ta Karyata Tattaunawa Da Washington Afrika
Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida Afrika
ACReSAL Ta Tallafa Wa FMC Kumo, Ta Shuka Bishiyoyi Tare Da Gyara Magudanan Ruwa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Hukumar NAHCON Ya Yabawa ‘Yan Jarida Kiwon Lafiya
  • Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
  • Yunkurin Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi Na Kara Kankama A Najeriya Labarai
  • NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
  • Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON Wasanni
  • Senegal Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirka Afcon 2025. Wasanni
  • CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025 Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.