Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON
Published: January 18, 2026 at 10:12 AM | By: Bala Hassan | Updated: January 18, 2026

Gwamnatin Tarayya ta taya Super Eagles murna bisa samun lambar tagulla a gasar AFCON.

Gwamnatin Tarayya ta taya ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Super Eagles murna bisa samun lambar yabo ta tagulla a gasar Kofin Nahiyar Afrika (AFCON) ta 2025, inda ta bayyana rawar da ƙungiyar ta taka a matsayin abin alfahari da farin ciki ga ’yan Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Asabar, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jinjina wa ‘yan ƙungiyar bisa yadda suka ɗaukaka tarihin ƙwallon ƙafa na Nijeriya da zuciya ɗaya, ƙwarewa, da jajircewa a tsawon gasar.

A cewar Ministan, Super Eagles sun nuna jarumta, haɗin kai, da amincewa da juna tun daga matakin rukunoni har zuwa busar ƙarshe a birnin Kasablanca na ƙasar Marokko, wanda hakan ya zaburar da miliyoyin ‘yan Nijeriya a gida da kuma ƙasashen waje.

Ya bayyana cewa irin wasan da suka yi ya wuce kawai buga ƙwallo, domin ya farfaɗo da kishin ƙasa da kuma kyakkyawar fata.

Ministan ya ce samun lambar tagulla ya sake ƙara wa tarihin nasarorin Nijeriya armashi a gasar AFCON, tare da ƙarfafa martabar da Super Eagles ke da ita a nahiyar.

Ya yaba wa ladabi da ruhin gwagwarmaya na ƙungiyar, musamman a wasannin da suka fafata da gaggan ƙungiyoyi.

Haka kuma, ya miƙa godiyar sa ga masu horaswa, ma’aikatan tallafi, da ‘yan wasan bisa sadaukarwa da jajircewar su duk da ƙalubalen da suka fuskanta.

Ya jaddada cewa wasan nasu ya nuna muhimmancin aiki tare, imani, da alfahari wajen wakiltar Nijeriya, ya ƙara da cewa wannan ƙoƙari ya sake tabbatar da matsayin Nijeriya a matsayin babbar ƙasa a ƙwallon ƙafar Afrika.

Ko da yake ya bayyana cewa babban kofin ta suɓuce musu a wannan karo, Ministan ya jaddada cewa an samu lambar tagullar cikin mutunci da ƙoƙari, kuma ba ta ‘yan wasan ba ce kawai, har ma ta ɗaukacin ‘yan Nijeriya ce waɗanda suka ba su goyon baya kuma suka yi imani da su a duk tsawon gasar.

Ya buƙaci Super Eagles da su yi murnar wannan nasara cikin alfahari, tare da ɗaukar ta a matsayin abin ƙarfafa gwiwa domin tunkarar duk wani ƙalubale nan gaba, sannan ya nuna godiya da jinjina kan yadda suka wakilci ƙasar nan.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya
Next Post: ADC Ta Sha Damarar Gwabzawa Da APC A Zaben 2027

Karin Labarai Masu Alaka

Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika
Real Madrid: Ta Kori Xabi Alonso Bayan Rashin Nasara A Wasan Kofin Sfaniya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026 Wasanni
An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa Wasanni
An Gudanar Da Taron Matasan Kasashe 6, Don Kawo Karshen Ta’addanci Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Ta Tasa Keyar Wani Jirgi Shake Da Mai Sauran Duniya
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
  • Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
  • Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
  • FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.