Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON
Published: January 18, 2026 at 10:12 AM | By: Bala Hassan | Updated: January 18, 2026

Gwamnatin Tarayya ta taya Super Eagles murna bisa samun lambar tagulla a gasar AFCON.

Gwamnatin Tarayya ta taya ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Super Eagles murna bisa samun lambar yabo ta tagulla a gasar Kofin Nahiyar Afrika (AFCON) ta 2025, inda ta bayyana rawar da ƙungiyar ta taka a matsayin abin alfahari da farin ciki ga ’yan Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Asabar, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jinjina wa ‘yan ƙungiyar bisa yadda suka ɗaukaka tarihin ƙwallon ƙafa na Nijeriya da zuciya ɗaya, ƙwarewa, da jajircewa a tsawon gasar.

A cewar Ministan, Super Eagles sun nuna jarumta, haɗin kai, da amincewa da juna tun daga matakin rukunoni har zuwa busar ƙarshe a birnin Kasablanca na ƙasar Marokko, wanda hakan ya zaburar da miliyoyin ‘yan Nijeriya a gida da kuma ƙasashen waje.

Ya bayyana cewa irin wasan da suka yi ya wuce kawai buga ƙwallo, domin ya farfaɗo da kishin ƙasa da kuma kyakkyawar fata.

Ministan ya ce samun lambar tagulla ya sake ƙara wa tarihin nasarorin Nijeriya armashi a gasar AFCON, tare da ƙarfafa martabar da Super Eagles ke da ita a nahiyar.

Ya yaba wa ladabi da ruhin gwagwarmaya na ƙungiyar, musamman a wasannin da suka fafata da gaggan ƙungiyoyi.

Haka kuma, ya miƙa godiyar sa ga masu horaswa, ma’aikatan tallafi, da ‘yan wasan bisa sadaukarwa da jajircewar su duk da ƙalubalen da suka fuskanta.

Ya jaddada cewa wasan nasu ya nuna muhimmancin aiki tare, imani, da alfahari wajen wakiltar Nijeriya, ya ƙara da cewa wannan ƙoƙari ya sake tabbatar da matsayin Nijeriya a matsayin babbar ƙasa a ƙwallon ƙafar Afrika.

Ko da yake ya bayyana cewa babban kofin ta suɓuce musu a wannan karo, Ministan ya jaddada cewa an samu lambar tagullar cikin mutunci da ƙoƙari, kuma ba ta ‘yan wasan ba ce kawai, har ma ta ɗaukacin ‘yan Nijeriya ce waɗanda suka ba su goyon baya kuma suka yi imani da su a duk tsawon gasar.

Ya buƙaci Super Eagles da su yi murnar wannan nasara cikin alfahari, tare da ɗaukar ta a matsayin abin ƙarfafa gwiwa domin tunkarar duk wani ƙalubale nan gaba, sannan ya nuna godiya da jinjina kan yadda suka wakilci ƙasar nan.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya
Next Post: ADC Ta Sha Damarar Gwabzawa Da APC A Zaben 2027

Karin Labarai Masu Alaka

Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora Wasanni
Arsenal Ba Ta Cikin Tattaunawa Kan Sayen Osimhen Wasanni
An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025. Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • CNG Ta Farfado Da Jarin Masu Adaidaita Sahu A Kaduna Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
  • Prime Ministan Senegal Ya Bayyana Shirin Sauya Sheka Afrika
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
  • Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed Labarai
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yansandan Uganda Sun Tsare ‘Yar Fafutukar Kare Hakkin Bil’adama Sarah Bireete Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Arsenal Ta Fara Kare Kambun Gasar Premier League Da Ci 3-0 A Kan Coventry City Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.