Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya
Published: January 18, 2026 at 9:13 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 18, 2026

Mutane 38 Sun Mutu, 218 Sun Jikkata a Wata Ɗaya Sakamakon Hatsarurrukan Mota.

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa, FRSC, reshen jihar Gombe, ta ce ta samu rahoton hatsarurrukan mota 38 tsakanin ranar 15 ga Disamba, 2025, zuwa 15 ga Janairu, 2026.

A cewar hukumar, hatsarurrukan sun shafi motoci 74 tare da shafar mutane 345, Daga cikin adadin, mutane 218 sun samu raunuka daban-daban, yayin da mutane 38 suka rasa rayukansu.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Route Commander Janet Kassa, ta fitar a madadin Kwamandan Sashen jihar, Samson Kaura, kuma aka bai wa manema labarai a Gombe.

Sanarwar ta danganta mafi yawan hatsarurrukan da kuskuren ɗan Adam da kuma matsalolin injunan mota, ciki har da ɗaukar kaya ko fasinjoji fiye da ƙima, gudu ba bisa ƙa’ida ba, gajiyar direba, da tuƙi a ƙarƙashin tasirin ƙwayoyi.

Sauran abubuwan da suka taimaka wajen faruwar hatsarurrukan sun haɗa da lalacewar tayoyi, matsalar birki, da rashin isasshen haske, kayan tsaro, ko kuma alamomin hanya.

Hukumar ta yi kira ga direbobi da su guji tuƙin ganganci, amfani da wayar hannu yayin tuƙi, tafiya saɓanin hanya, da duk wani abu da ke iya daukar hankalinsu daga kan hanya.

Da take jaddada cewa kiyaye lafiya nauyi ne na kowa da kowa, Janet Kassa ta ce dole ne direbobi su daina tuƙi cikin sakaci.

Hukumar ta kuma tabbatar da ƙudirin ta na rage yawan hatsarurrukan mota zuwa mafi ƙarancin mataki.

A cewar sanarwar, “FRSC na ci gaba da aiwatar da ayyukanta na tabbatar da hanyoyi masu aminci a jihar Gombe ta hanyar sintiri na yau da kullum, cire cikas a kan hanya, ayyukan ceto, da wayar da kan jama’a a tashoshin mota da wuraren ibada.”

Hukumar ta lura cewa ƙarshen shekara da farkon sabuwar shekara na daga cikin lokutan da ake samun yawaitar zirga-zirga sakamakon ƙaruwa a harkokin jama’a, lamarin da galibi ke zuwa da barazana ga rayuka da kuma tattalin arziki.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: An Kashe Mutane 7 A Unguwar Dorayi Dake Kano
Next Post: Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON

Karin Labarai Masu Alaka

An Gurfaranar Da Wadanda Ake Zargi Takai Hari Gaban Kotu Najeriya
An Kashe Sojojin Bangladesh A Kasar Sudan Tsaro
Sanata Goje Yayi Watsi Da Fidda ‘Yan Takarar APC A Gombe Afrika
‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
Isra’ila Zata Rusa Gidajen Da Suke Iyakarta Da Lebanon Labarai
Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal Ya Bar PDP Ya Koma APC Labarai
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane Takwas Da Ake Zargi Da Siyar Da Tikitin AFCON Ba Bisa Ka’ida Ba Wasanni
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
  • Amurka Tace Zata Gama Yakin Iran Cikin Makonni Afrika
  • Kungiyar HPV A Jihar Gombe Ta Jagoranci Yaki Da Karuwar Cutar Daji Afrika
  • Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi Labarai
  • Kasar China Ta Daina Bada Bashi Da Dalar Amurka Sai Da Kudin Kasar Yuan Labarai
  • Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.