Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Netanyahu Yana Neman Shawarwari Daga Hukumomin Lebanon
Published: April 10, 2026 at 5:23 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Prime Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya fada jiya Alhamis cewa, yana neman shawarwari kai tsaye da hukumomin Lebanon a Beiruit, kwana daya bayan da Isra’ila ta kai hari mafi muni da bama-bamai tun fara yakin, har ta halaka mutane dari uku, wanda ya jefa yarjejeniyar tsagaita wuta da shugaba Donald Trump ya kulla da Iran, cikin hadari.

Wani jami’in Lebanon ya gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, ita ma Lebanon tana bukatar ta gudanar da shawarwari kai tsaye da Isra’ila na neman a tsagaita wuta, shigen abunda yake gudana tsakanin Iran da Amurka.

Trump ya bayyana shirin tsagaita wuta a yakin hadin guiwar Amurka da Isra’ila kan Iran da ya shiga mako shida, a daren talata, jim kadan kamin wa’adin da ya bayar ya kure, wanda yayi barazanar zai shafe Iran daga doron kasa.

A Pakistan, hukumomin kasar suna shirye shiryen zaman farko na shawarwari tsakanin Amurka da Iran, tuni har ta rufe wasu hanyoyi a Isalamabad babban birnin kasar.

Sai dai babu wata alamar cewa Iran ta bude mashigin ruwan Hormuz, matakin da ya janyo mummunar kassara jigilar makamashi a tarihi, inda Tehran take nuni da ci gaban hare hare da isra’ila take kai wa a Lebanon , a zaman dalili.

A cikin sa’o’i 24 tun bayan sanarda tsagaita wuta, jirgin ruwa mai dakon daya ne kadai, tare da wasu jirage masu dakon kaya 5 ne suka ratsa ta mashigin ruwa na Hormuz, hanyar da galibi jiragen ruwa 140 suke bi ako wace rana, inda ta nan ne kashi 20 cikin dari na makamashi da duniya ta dogara akai yake bi.

Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sakataren Kungiyar NATO Yayi Magana Da Hukumomin Kasashe
Next Post: Birtaniya Zata Hana Jiragen Ruwan Rasha Wucewa

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Spain Zata Bada Diyya Ga Iyalen Wadanda Da Suka Rasu A Hatsarin Jirgin Kasa Labarai
Shugabar Kungiyar Cinikayya Ta Duniya Ta Bukaci Kasashe Su Gyara Harkokin Cinikayya Afrika
Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka Amurka
Damara Ya Tallafa Wa Gasar Karatun Al-Qur’ani Da Naira Miliyan Biyar A Bambam Afrika
Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv Afrika
Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya Wasanni
  • Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe Siyasa
  • Dakarun Zaman Lafiya Na Majalisar Dinkin Duniya Sun Rasa Rayukan Su Afrika
  • Bayan Shafe Shekaru Hudu A Mulki Sarkin Hausawan Ibadan Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sabon Jadawalin Gasar Kwalon Kafa Ta Turai 2026 Wasanni
  • Sakataren Gwamnatin Amurka Ya Bayyana Bawa Kungiyoyin Agaji Damar Kai Taimako Sudan Amurka
  • Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako Labarai
  • Zulum Ya Jinjinawa Hadiza Aliyu Kan Naɗin Ta A Matsayin Babbar Editar NAN Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.