Dan siyasar nan, Jerry Joseph Damara, ya bayar da tallafin naira miliyan biyar domin tallafa wa taron karatun Al-Qur’ani na shekara-shekara da ƙungiyar Izala ke gudanarwa a garin Bambam, ƙaramar hukumar Balanga ta jihar Gombe dake arewa maso Gabashin Najeriya
Damara ya bayar da tallafin ne yayin da ya halarci taron addinin, inda ya bayyana karatun Al-Qur’ani a matsayin muhimmin aiki na ibada da ke ƙarfafa kyawawan ɗabi’u, zaman lafiya da haɗin kan al’umma.
Ya ce tallafin nasa ya nuna yadda yake ƙoƙarin inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban, tare da kula da jin daɗin al’ummar da yake wakilta ba tare da la’akari da bambancin addini ba.
Damara ya kuma tabbatar wa al’ummar Balanga cewa zai ci gaba da jajircewa wajen samar da ci gaba mai ɗauke da kowa, yana mai cewa wakilcinsa zai mayar da hankali ne kan ayyuka da shirye-shiryen da za su inganta rayuwar al’umma.
Shugabannin al’umma da malaman addinin Musulunci da suka halarci taron sun yaba da tallafin, inda suka bayyana shi a matsayin abin da ya zo a lokacin da ya dace kuma mai karimci.
Sun yi kira ga sauran masu ruwa da tsaki da masu rike da mukaman gwamnati da su yi koyi da irin wannan hali na tallafa wa ayyukan da ke inganta rayuwar ruhaniya da zamantakewar al’umma.
An kuma gudanar da addu’o’i domin samun zaman lafiya, ci gaba da wadata a Najeriya, tare da roƙon Allah Ya ci gaba da ba Damara nasara a ayyukan da yake yi wa al’umma.
Daga cikin manyan baki da suka halarci taron akwai Sakataren Gwamnatin Jihar Gombe, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi; ‘yar takarar jam’iyyar APC a mazabar tarayya ta Kaltungo/Shongom, Hajiya Fatima Binta Bello; tsohon mataimakin gwamnan jihar, Thaanda Jason Rubainu; da mai bai wa Gwamna shawara kan harkokin ƙarfafa matasa, Iliya Suleiman, da sauran baki.


