Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya
Published: December 18, 2025 at 11:33 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Gwamnatin Jihar Adamawa aa amince da naira Biliyan 583.3 a matsayin kasafin kuɗi na shekarar 2026.
Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, da majalisar shi ta amince da tsarin kasafin kuɗi na naira biliyan 583,331,380,496, a 2026, wanda aka yi wa take da “Kasafin Ci Gaba Mai Ɗorewa da Sabuntawa”.
Kasafin ya tanadi naira biliyan 209.64 (kashi 35.93) a matsayin kuɗaɗen gudanarwa, yayin da za a kashe naira biliyan 373.69, (kashi 64.07) kan ayyukan raya ƙasa, abin da ke nuni da fifikon da gwamnati ta bai wa manyan ayyukan ci gaba.
A zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar da Mataimakiyar Gwamna, Farfesa Kaletapwa G. Farauta, ta jagoranta, majalissar ta kuma jajanta wa al’ummar Karamar Hukumar Lamurɗe, tare da kira ga jama’a da su rungumi zaman lafiya da haɗin kai. Haka kuma, an shawarci al’umma da su kasance masu lura da tsaro ta hanyar gano baƙi a cikin unguwanninsu.
Daga cikin muhimman ayyukan da aka amince da su akwai gina cikakkun filayen wasanni a Kwalejin Fasaha, Ƙirƙira da Nazarin Kasuwanci da ke Gulak kan kuɗin Naira Biliyan 1.78; da kuma gina Ginin Babbar Kotun Jiha a Gulak, Karamar Hukumar Madagali, kan Naira Miliyan 373.77, da wa’adin kammalawa na watanni shida.
Majalisar ta kuma amince da gina Sakatariyar Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Jihar Adamawa a kan Naira Biliyan 2.50, wadda za a kammala cikin watanni 12. Sauran ayyukan sun haɗa da gina hanyar kilomita 2.2 daga Sangere Bode zuwa wasu matsugunnai a Yola South kan Naira Miliyan 290.31, da kuma hanya mai nisan kilomita 8.5 daga titin Numan zuwa Jalingo zuwa Kodomti da Shaforon a kan Naira Biliyan 1.89.
Haka zalika, gwamnatin ta amince da aikin gina katangar bulo ta Jami’ar Jihar Adamawa, Mubi, a kan kuɗin Naira Biliyan 3.53.
Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati
Next Post: Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Faransa Da Italiya Sun Nuna Rashin Amincewa Da Matakan Sojoji Amurka
Pakistan Zata Karbi Tattaunawar Rikicin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Farfesa Inuwa Ja’afaru Yakarbi Ragamar Shugabancin Jami’ar Kashere Labarai
Jami’an Shiga Da Fice A Afirka Ta Kudu Sun Tafka Badakalar Kudade Afrika
Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
Iran Tana Duba Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Amurka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Pakistan Zata Karbi Tattaunawar Rikicin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • NAHCON Tafara Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026 Najeriya
  • An Canza Shugabannin Hukumar Hakar Ma’adanai A Congo Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
  • Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika
  • Manoma Suna Fuskantar Barazanar Karyewa A Kasar Ghana Afrika
  • Tinubu Na Kokarin Rage Tsadar Sufuri Ta Hanyar Shirin CNG Afrika
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.