Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Pakistan Zata Karbi Tattaunawar Rikicin Gabas Ta Tsakiya
Published: March 30, 2026 at 9:26 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ƙasar Pakistan ta bayyana a ranar Lahadi cewa tana shirin karɓar bakuncin “tattaunawa masu ma’ana” domin kawo ƙarshen rikicin da ya shafi Iran nan da kwanaki masu zuwa, duk da cewa a baya Tehran ta zargi Amurka da shirya kai farmakin ƙasa yayin da take neman tattaunawa.

Da yake magana bayan ganawar ministocin harkokin wajen yankin, Ministan Harkokin Wajen Pakistan, Ishaq Dar, ya ce sun tattauna hanyoyin da za su iya kawo ƙarshen yaƙin cikin gaggawa da kuma na dindindin a yankin, tare da yiwuwar tattaunawa tsakanin Amurka da Iran a birnin Islamabad.

Ya ce: “Pakistan za ta ji daɗin karɓar bakunci tare da sauƙaƙa tattaunawa masu ma’ana tsakanin ɓangarorin biyu nan da kwanaki masu zuwa, domin cimma cikakkiyar sulhu mai ɗorewa kan rikicin da ke gudana.” Sai dai ba a bayyana ko Amurka da Iran sun amince za su halarci tattaunawar ba.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka da White House ba su bayar da amsa nan take ba kan bukatar yin tsokaci game da yiwuwar tattaunawar a Pakistan.

A baya, Kakakin Majalisar Dokokin Iran, Mohammad Baqer Qalibaf, ya zargi Amurka da aikewa da saƙonnin tattaunawa yayin da a lokaci guda take shirin tura sojoji, yana mai ƙara da cewa Tehran a shirye take ta mayar da martani idan aka tura sojojin Amurka.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon
Next Post: Fafaroma Leo Yayi Allah Wadai Bisa Karuwar Yake Yaken Gabas Ta Tsakiya

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri Amurka
Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran Afrika
Majalisar Dattawan Amurka Ta Amince Da Wata Doka Amurka
Ingila, Hauhawar Farashi Yayi ƙasa Sosai Labarai
Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438 Labarai
Fiye Da Fararen Hula 1000 Yunwa Ta Kashe A Sudan Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Saied Yana Cigaba Da Samun Goyon Bayan Al’ummar Kasar Tunisiya Afrika
  • Gwamnatin Tinubu Zata Samar Da Wutan Solar A Jami’ar ADUST Wudil Afrika
  • Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
  • Sojojin Amurka Sun Isa Najeriya Don Yaki Da Ta’addanci Amurka
  • Shugabannin Kiristocin Arewa Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Ummulkhairi Afrika
  • An Bude Kamfanin Sarrafa Ma’adanai A Kasar Mozambique Labarai
  • EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
  • Karamar Sallah: Hukumar Kashe Gobara A Gombe Ta Kuduri Aniyar Kare Al’umma Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.