Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438
Published: December 28, 2025 at 6:14 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar Tsaron haɗin gwiwa ta Arewa maso Gabashin Najeriya, Operation Hadin Kai (OPHK), ta kashe ‘yan ta’adda 438 na Boko Haram da ISWAP cikin watanni bakwai.

Kwamandan rundunar OPHK a yankin Arewa maso Gabas, Sashi na daya, Manjo Janar Abdulsalam Abubakar, ne ya bayyana hakan a ranar Asabar yayin liyafar Kirsimeti da aka gudanar a Maiduguri, inda ya ce an gudanar da ayyukan ne tsakanin watan Mayu da Disamba.

Abubakar ya ce jami’an rundunar sun kuma ƙwato makamai iri-iri 254, na’urorin sadarwa na Starlink guda 300, tare da ceto fararen hula 366 daga maboyar ‘yan ta’adda daban-daban.

Ya ce, Mika wuya da ‘yan ta’adda 881 na JAS/ISWAP tare da iyalan su, na daga cikin manyan nasarorin da suka nuna ci gaban da aka samu.

Janar ɗin sojan ya ƙara da cewa bikin Kirsimeti ya zo dai dai da ayyukan rundunar na lokacin rani a yankin.

Abubakar ya danganta nasarorin da aka samu a ayyukan haɗin gwiwar bisa ga samun goyon baya daga Babban Hafsan Sojojin Ƙasan Najeriya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Yau Lahadi Ake Gudanar Da Zabe A Kasar Myanmar
Next Post: Jamhuriyar Nijar Ta Fitar Da Doka Domin Kare ‘Yancin ‘Yan Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano Labarai
‘Yan Sanda A Tsibirin Bahamas Sun kama Mijin Wata Ba Amurkiya Amurka
Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika
Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai
Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya
  • Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato Afrika
  • Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan Labarai
  • Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe Afrika
  • Kamfanin Magani Na Aspen Yayi Gagarumar Asara A Cinikayya Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
  • Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.