Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438
Published: December 28, 2025 at 6:14 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar Tsaron haɗin gwiwa ta Arewa maso Gabashin Najeriya, Operation Hadin Kai (OPHK), ta kashe ‘yan ta’adda 438 na Boko Haram da ISWAP cikin watanni bakwai.

Kwamandan rundunar OPHK a yankin Arewa maso Gabas, Sashi na daya, Manjo Janar Abdulsalam Abubakar, ne ya bayyana hakan a ranar Asabar yayin liyafar Kirsimeti da aka gudanar a Maiduguri, inda ya ce an gudanar da ayyukan ne tsakanin watan Mayu da Disamba.

Abubakar ya ce jami’an rundunar sun kuma ƙwato makamai iri-iri 254, na’urorin sadarwa na Starlink guda 300, tare da ceto fararen hula 366 daga maboyar ‘yan ta’adda daban-daban.

Ya ce, Mika wuya da ‘yan ta’adda 881 na JAS/ISWAP tare da iyalan su, na daga cikin manyan nasarorin da suka nuna ci gaban da aka samu.

Janar ɗin sojan ya ƙara da cewa bikin Kirsimeti ya zo dai dai da ayyukan rundunar na lokacin rani a yankin.

Abubakar ya danganta nasarorin da aka samu a ayyukan haɗin gwiwar bisa ga samun goyon baya daga Babban Hafsan Sojojin Ƙasan Najeriya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Yau Lahadi Ake Gudanar Da Zabe A Kasar Myanmar
Next Post: Jamhuriyar Nijar Ta Fitar Da Doka Domin Kare ‘Yancin ‘Yan Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar NAPTIP Ta Kubutar Da Yara 11 Daga Hannun Masu Safara Mutane Labarai
Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025 Labarai
Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya Labarai
Fargaba Ta Karu Duk Da Tsagaita Wuta Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tsarin Haraji Mai Cike Da Ayoyin Tambaya Na Shirin Fara Aiki Labarai
  • Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba Labarai
  • ‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
  • Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ya Kashe Mutane Biyar A Tanzaniya Afrika
  • Shugaba Trump Ya Janye Karbar Kudin Fito Daga Wasu Kasashen Turai Amurka
  • Sojojin Amurka Sun Kutsa Cikin Kasar Iran Labarai
  • Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
  • Afirka Ta Kudu Da Kenya Sun Bayyana Yaudarar ‘Yan Kasashe Da Yawa Tare Da Sakasu Yaki Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.