Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025
Published: January 16, 2026 at 8:26 AM | By: Bala Hassan

An dakatar da tsohon tauraron kwallon kafa na Kamaru Samuel Eto’o na wasanni hudu tare da cin tararsa dala $20,000 (£14,960) bayan kwamitin ladabtarwa na Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (Caf) ya same shi da laifin rashin da’a.

Sanarwar Caf ta ce Eto’o, wanda yanzu shine shugaban hukumar kwallon kafa ta kasarsa Kamaru (Fecafoot), ya karya ka’idojinta na wasanni a lokacin wasan kusa da na karshe na gasar cin kofin kasashen Afirka ta 2025 tsakanin Kamaru da Morocco.

An ruwaito cewa tsohon dan wasan gaban Barcelona da Inter Milan ya nuna fushinsa kan wasu daga cikin shawarwarin da jami’an suka yanke yayin da Indomitable Lions ta sha kashi 2-0 a hannun masu masaukin baki Ƙasar Moroko.

Shugaban Caf Patrice Motsepe, wanda shi ma ya halarci filin wasa da ke Rabat, ya shaida faruwar abun inda ya nuna takaicin sa ga me da Eto’o.

A ranar Litinin hukumar gudanarwa ta nahiyar ta sanar da fara bincike kan “tashin hankali da kuma halayyar da ba a yarda da ita ba ta wasu ‘yan wasa da jami’ai” a wasannin ƙungiyoyi takwas na gasar ta AFCON.

A martanin da ta mayar, hukumar kwallon kafa ta Kamaru Fecafoot ta yi watsi da matakin na Caf, inda ta bayyana tsarin amatsayin abun shakku game da buƙatan shari’a mai adalci”.

Sannan Fecafoot ta nuna goyon bayanta ga shugabanta a cikin wata sanarwa a ranar Laraba, yayin da ta nuna cewa Eto’o zai daukaka kara kan hukuncin.

Tun bayan da ya hau kan mukaminsa a shekarar 2021, an lalata tasirin Eto’o a matsayin gwarzon wasan saboda wasu hayaniya da ke da alaka da badakala da matsaniya.

Inda ya fuskanci zarge-zargen rashin da’a da rashin kyakkyawan shugabanci, wasu masu ruwa da tsaki a kwallon kafa suma ke korafin manyan kura-kurai a cikin Fecafoot.

A yayin tantance ‘yan wasa da zasu wakilci Ƙasar Kamaru a gasar cin kofin kasashen Afirka da ke guda na a Moroko an zargi Eto’o da sanya baki wajan kawo sunayen wadda ya ke so yayin da ya ceri wadda ake ganin basa shiri irin su maitsaron ragar Manchester United Andrew Onana, da Vincent Abubakar.

Sai dai Eto’o ya sha musanta irin wadannan zarge-zargen, yana mai bayyana nasarorin da aka samu a matsayin shugaban Hukumar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Trump Ta Karawa Iran Wasu Takunkumai
Next Post: Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar Ya Shiga Jam’iyyar APC

Karin Labarai Masu Alaka

Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala Afrika
Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar Afrika
SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai
APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasashen Faransa Da Italiya Sun Nuna Rashin Amincewa Da Matakan Sojoji Amurka
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Taki Da Mai Ga Manoma Labarai
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno Tsaro
  • An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa Tsaro
  • ‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.