Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne
Published: December 17, 2025 at 7:21 PM | By: Bala Hassan

An kama wani Mutum da ake zargi ɗan damfara ne da yake zaluntar masu jinya a Asibiti ATBUTH Bauchi 

Wata takarda da aka rabawa manema labarai ya tabbatar da cewa sashen SERVICOM na Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke tarayyar Najeriya a jihar Bauchi, ya danke wani mani Mutum da ake zargin ɗan damfara ne da yake damfarar wadda suka zo jinya a asibitin da danginsu a cikin haraba.

Bayanan na cewar an kama mutumin ne a lokacin wani aikin surru da akayi cikin dare kamar yadda aka saba yi a wasu lokuta, inda aka same wadda ake zargin ya karbi naira dubu 45, daga dangin wani majinyaci da yake samun kulawa sakamakon raunin harbin bindiga.

 

 

 

 

 

 

 

A cewar sanarwar  dauke da sahanun Jami’in Hulda da Jama’a na ATBUTH, Usman Abdullahi Koli tace wanda ake zargin ya nemi a bashi Naira 5,000, a matsayin kuɗin katin asibiti sai kuma Naira 40,000, don sayan magunguna.

Koli, yace ainihin kudin katin asibitin Naira 1,000, ne yayin da kuɗin magungunan suka kai Naira 18,150.

Sai dai an karɓi sauran Naira 27,000 daga hannun wanda ake zargin, inda daga bisani aka mika shi ga hukumar ‘yan sanda don cigaba da bincike da kuma gurfanar da shi a gaban shari’a.

Da yake tsokaci dangane da wannan faruwar wannan lamarin, Shugaban asibitin ATBUTH, Farfesa Yusuf Jibrin Bara, ya yaba wa tawagar ta SERVICOM bisa kokarin su na gano wannan mumunar barnan da kuma sanya ido da suka yi, daga bisani ya sake nanata manufar hukumar asibitin na yaƙi da cin hanci da zamba, kutse a aikin jami’a, da sauran munanan ayyuka.

Inda ya bukaci marasa lafiya da jama’a da su kasance masu lura da al’uman da zasu zo musu da niyar zasu taimakesu, da su gaggauta kai rahoton duk mutanen da basu yarda da shi ba, ko kuma bukatar biyan kudi ba bisa ka’ida ba zuwa ofishin SERVICOM ko su nemi hukumomin asibiti.

Farfesa Bara ya ce yana mai tabbatar da cewa hukumar gudanarwa za ta ci gaba da karfafa hanyoyin sa ido don kare majinyanta da tabbatar da gaskiya a asibitin.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe
Next Post: Ingila, Hauhawar Farashi Yayi ƙasa Sosai

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Zata Kara Tura Sojoji Gabas Ta Tsakiya Afrika
UNICEF Ta Tallafawa Jihar Bauchi Da Babura Afrika
Kasar Amurka Tabada Tabbacin Bawa Ukraine Tsaron Shekarun 15 Amurka
Shugaban Ƙasar Koriya Ta Arewa Ya Halarci Gwajin Makami Mai Linzamin Kasar Labarai
Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe Amurka
Hukumar EFCC Ta Kama Dan Kasuwa A Kamaru Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
  • An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
  • Samar Da Albarkatun Mai Ya Ragu A Iraq Afrika
  • Amurkawa Suna Turuwa Zuwa Kasar Faransa Duk Da Rashin Jituwa A Tsakanin Kasashen Amurka
  • Kasuwannin Hannun Jari Sun Farfado Afrika
  • ‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka  Labarai
  • Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
  • Sojoji Zasu Taimakawa ‘Yan Sanda Wajen Yaki Da Mugayen Ayyuka Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.