Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne
Published: December 17, 2025 at 7:21 PM | By: Bala Hassan

An kama wani Mutum da ake zargi ɗan damfara ne da yake zaluntar masu jinya a Asibiti ATBUTH Bauchi 

Wata takarda da aka rabawa manema labarai ya tabbatar da cewa sashen SERVICOM na Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke tarayyar Najeriya a jihar Bauchi, ya danke wani mani Mutum da ake zargin ɗan damfara ne da yake damfarar wadda suka zo jinya a asibitin da danginsu a cikin haraba.

Bayanan na cewar an kama mutumin ne a lokacin wani aikin surru da akayi cikin dare kamar yadda aka saba yi a wasu lokuta, inda aka same wadda ake zargin ya karbi naira dubu 45, daga dangin wani majinyaci da yake samun kulawa sakamakon raunin harbin bindiga.

 

 

 

 

 

 

 

A cewar sanarwar  dauke da sahanun Jami’in Hulda da Jama’a na ATBUTH, Usman Abdullahi Koli tace wanda ake zargin ya nemi a bashi Naira 5,000, a matsayin kuɗin katin asibiti sai kuma Naira 40,000, don sayan magunguna.

Koli, yace ainihin kudin katin asibitin Naira 1,000, ne yayin da kuɗin magungunan suka kai Naira 18,150.

Sai dai an karɓi sauran Naira 27,000 daga hannun wanda ake zargin, inda daga bisani aka mika shi ga hukumar ‘yan sanda don cigaba da bincike da kuma gurfanar da shi a gaban shari’a.

Da yake tsokaci dangane da wannan faruwar wannan lamarin, Shugaban asibitin ATBUTH, Farfesa Yusuf Jibrin Bara, ya yaba wa tawagar ta SERVICOM bisa kokarin su na gano wannan mumunar barnan da kuma sanya ido da suka yi, daga bisani ya sake nanata manufar hukumar asibitin na yaƙi da cin hanci da zamba, kutse a aikin jami’a, da sauran munanan ayyuka.

Inda ya bukaci marasa lafiya da jama’a da su kasance masu lura da al’uman da zasu zo musu da niyar zasu taimakesu, da su gaggauta kai rahoton duk mutanen da basu yarda da shi ba, ko kuma bukatar biyan kudi ba bisa ka’ida ba zuwa ofishin SERVICOM ko su nemi hukumomin asibiti.

Farfesa Bara ya ce yana mai tabbatar da cewa hukumar gudanarwa za ta ci gaba da karfafa hanyoyin sa ido don kare majinyanta da tabbatar da gaskiya a asibitin.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe
Next Post: Ingila, Hauhawar Farashi Yayi ƙasa Sosai

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai
‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Gaddafi A Gidansa Dake Kasar Libya Afrika
Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno Afrika
Kamfanin Magani Na Aspen Yayi Gagarumar Asara A Cinikayya Afrika
Kungiyar Cigaban Al’ummar Tangale Tace Bata Goyon Bayan Kai Ziyara Wa Gwamnan Gombe Labarai
Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
  • Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Zata Binciki Kasar Iran Afrika
  • Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Trump Da Gwamnan Minnesota Zasu Sassautawa Bakin Haure Amurka
  • Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
  • Yunkurin Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi Na Kara Kankama A Najeriya Labarai
  • Magoya Bayan Tijjaniyya Zasu Kauracewa Zabe Saboda Kama Sheikh Sani Khalifa Afrika
  • Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.