Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne
Published: December 17, 2025 at 7:21 PM | By: Bala Hassan

An kama wani Mutum da ake zargi ɗan damfara ne da yake zaluntar masu jinya a Asibiti ATBUTH Bauchi 

Wata takarda da aka rabawa manema labarai ya tabbatar da cewa sashen SERVICOM na Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke tarayyar Najeriya a jihar Bauchi, ya danke wani mani Mutum da ake zargin ɗan damfara ne da yake damfarar wadda suka zo jinya a asibitin da danginsu a cikin haraba.

Bayanan na cewar an kama mutumin ne a lokacin wani aikin surru da akayi cikin dare kamar yadda aka saba yi a wasu lokuta, inda aka same wadda ake zargin ya karbi naira dubu 45, daga dangin wani majinyaci da yake samun kulawa sakamakon raunin harbin bindiga.

 

 

 

 

 

 

 

A cewar sanarwar  dauke da sahanun Jami’in Hulda da Jama’a na ATBUTH, Usman Abdullahi Koli tace wanda ake zargin ya nemi a bashi Naira 5,000, a matsayin kuɗin katin asibiti sai kuma Naira 40,000, don sayan magunguna.

Koli, yace ainihin kudin katin asibitin Naira 1,000, ne yayin da kuɗin magungunan suka kai Naira 18,150.

Sai dai an karɓi sauran Naira 27,000 daga hannun wanda ake zargin, inda daga bisani aka mika shi ga hukumar ‘yan sanda don cigaba da bincike da kuma gurfanar da shi a gaban shari’a.

Da yake tsokaci dangane da wannan faruwar wannan lamarin, Shugaban asibitin ATBUTH, Farfesa Yusuf Jibrin Bara, ya yaba wa tawagar ta SERVICOM bisa kokarin su na gano wannan mumunar barnan da kuma sanya ido da suka yi, daga bisani ya sake nanata manufar hukumar asibitin na yaƙi da cin hanci da zamba, kutse a aikin jami’a, da sauran munanan ayyuka.

Inda ya bukaci marasa lafiya da jama’a da su kasance masu lura da al’uman da zasu zo musu da niyar zasu taimakesu, da su gaggauta kai rahoton duk mutanen da basu yarda da shi ba, ko kuma bukatar biyan kudi ba bisa ka’ida ba zuwa ofishin SERVICOM ko su nemi hukumomin asibiti.

Farfesa Bara ya ce yana mai tabbatar da cewa hukumar gudanarwa za ta ci gaba da karfafa hanyoyin sa ido don kare majinyanta da tabbatar da gaskiya a asibitin.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe
Next Post: Ingila, Hauhawar Farashi Yayi ƙasa Sosai

Karin Labarai Masu Alaka

Dusar Kankara Ta Hana Jirage Tashi A Birnin Paris Labarai
Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026 Labarai
Yaki Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Ya Shiga Kwana Na Biyar Afrika
Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika
Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye Afrika
Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
  • Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
  • Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas Labarai
  • Jaura Ta Bayyana A Wasu Jihohin Amurka Labarai
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
  • Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.