Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Hukumar Raya Birane Ta Rushe Gine-Ginen Da Suka Keta Dokokin Tsara Birane A Gombe
Published: June 14, 2026 at 10:05 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar Tsare-tsare da Raya Birane ta Jihar Gombe (GOSUPDA) ta ƙara ƙaimi wajen aiwatar da dokokin tsara birane, inda ta rushe wasu gine-gine da shagunan kasuwanci da aka gina ba bisa ka’ida ba a kan titin tsohon Mile uku da sauran sassan birnin Gombe.

Matakin ya biyo bayan jerin sanarwar rusau da gargaɗi da hukumar ta bai wa masu mallakar gine-ginen da abin ya shafa, tana mai umartar su da su bi dokokin tsara birane tare da cire gine-ginen da aka yi ba tare da izini ba.

Da yake magana yayin aikin rusau ɗin, Shugaban Hukumar, Alhaji Bappayo Samanja Maudo ya bayyana cewa matakin wani ɓangare ne na ƙoƙarin da gwamnati ke yi na dawo da tsari a babban birnin jihar, tabbatar da bin ƙa’idojin gine-gine da aka amince da su, da kuma bunƙasa ci gaban birane mai ɗorewa.

Daga cikin gine-ginen da aka rushe akwai wasu shagunan kasuwanci da ke gaban Gidan rediyon Gombe waɗanda rahotanni suka nuna cewa an gina su ba tare da sahalewar hukuma ba tsawon sama da shekaru goma.

Hukumar ta ce gine-ginen sun mamaye wuraren jama’a da aka tanada tare da karya ƙa’idojin raya birane da ake aiki da su.

Haka kuma, aikin ya shafi wani wurin sayar da kaji da wasu wuraren kasuwanci da aka gina ba bisa ƙa’ida ba a kusa da otel din Jiyamare da ke yankin Tsohon Mile uku a cikin birnin Gombe.

A cewar shugaban hukumar, an gina waɗannan wurare ba tare da samun takardun izinin gini da suka dace ba, lamarin da ke kawo cikas ga tsarin raya birnin da aka tsara.

Hukumar ta sake jaddada aniyarta ta kawar da duk wasu gine-ginen da aka yi ba bisa ƙa’ida ba a faɗin jihar, tare da gargaɗin mazauna jihar, masu zuba jari da masu gudanar da harkokin kasuwanci da su guji fara kowane aikin gini ba tare da samun amincewar hukumomin da abin ya shafa ba.

Ta kuma buƙaci al’umma su ba da haɗin kai ta hanyar bin dokokin tsara birane, tana mai jaddada cewa gine-ginen da ke da sahalewar hukuma kaɗai za a bari su ci gaba da kasancewa.

Hukumar ta ce manufar wannan aikin ita ce samar da muhalli mai tsari, tsaro da kyan gani ga al’ummar jihar Gombe.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa
Next Post: Anyi Bikin Cikar Tsohon Shugaban Kasa Abdulsalami Shekaru 84

Karin Labarai Masu Alaka

Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
Angano Gawar Wani Dan Myanmar A Arewacin New York Afrika
Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna Afrika
Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
Kasashen Daular Larabawa Tare Da Saudiya Da Jordan Sunyi Allah Wadai Da kasar Israel Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Guinea Bissau Ta Tsaida Gwaje-Gwajen Allurar Rigakafin Shawara A Kasar Labarai
  • Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
  • Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato Labarai
  • Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan Labarai
  • An Gudanar Da Tiyatar Ido Kyauta A Gombe Afrika
  • An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi Tsaro
  • Kauran Bauchi: Muna Nan A PDP Daram! Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.