Hukumar Tsare-tsare da Raya Birane ta Jihar Gombe (GOSUPDA) ta ƙara ƙaimi wajen aiwatar da dokokin tsara birane, inda ta rushe wasu gine-gine da shagunan kasuwanci da aka gina ba bisa ka’ida ba a kan titin tsohon Mile uku da sauran sassan birnin Gombe.
Matakin ya biyo bayan jerin sanarwar rusau da gargaɗi da hukumar ta bai wa masu mallakar gine-ginen da abin ya shafa, tana mai umartar su da su bi dokokin tsara birane tare da cire gine-ginen da aka yi ba tare da izini ba.
Da yake magana yayin aikin rusau ɗin, Shugaban Hukumar, Alhaji Bappayo Samanja Maudo ya bayyana cewa matakin wani ɓangare ne na ƙoƙarin da gwamnati ke yi na dawo da tsari a babban birnin jihar, tabbatar da bin ƙa’idojin gine-gine da aka amince da su, da kuma bunƙasa ci gaban birane mai ɗorewa.

Daga cikin gine-ginen da aka rushe akwai wasu shagunan kasuwanci da ke gaban Gidan rediyon Gombe waɗanda rahotanni suka nuna cewa an gina su ba tare da sahalewar hukuma ba tsawon sama da shekaru goma.

Hukumar ta ce gine-ginen sun mamaye wuraren jama’a da aka tanada tare da karya ƙa’idojin raya birane da ake aiki da su.
Haka kuma, aikin ya shafi wani wurin sayar da kaji da wasu wuraren kasuwanci da aka gina ba bisa ƙa’ida ba a kusa da otel din Jiyamare da ke yankin Tsohon Mile uku a cikin birnin Gombe.
A cewar shugaban hukumar, an gina waɗannan wurare ba tare da samun takardun izinin gini da suka dace ba, lamarin da ke kawo cikas ga tsarin raya birnin da aka tsara.

Hukumar ta sake jaddada aniyarta ta kawar da duk wasu gine-ginen da aka yi ba bisa ƙa’ida ba a faɗin jihar, tare da gargaɗin mazauna jihar, masu zuba jari da masu gudanar da harkokin kasuwanci da su guji fara kowane aikin gini ba tare da samun amincewar hukumomin da abin ya shafa ba.
Ta kuma buƙaci al’umma su ba da haɗin kai ta hanyar bin dokokin tsara birane, tana mai jaddada cewa gine-ginen da ke da sahalewar hukuma kaɗai za a bari su ci gaba da kasancewa.
Hukumar ta ce manufar wannan aikin ita ce samar da muhalli mai tsari, tsaro da kyan gani ga al’ummar jihar Gombe.


