Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC
Published: December 18, 2025 at 9:50 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 18, 2025

Ɗan takarar gwamnan jihar Gombe na jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Muhammad Jibrin Barde, ya fice daga PDP zuwa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) gabanin zaɓen 2027.

Dan Barde ya bayyana hakan a daren ranar Talata a gidansa, inda ya nuna katin zamowa mamba na ADC, yana mai cewa ya dawo ne domin sabunta rajistar sa da jama’rsa

Ya ce ya bar PDP tun farkon shekarar 2025, yana jaddada cewa burinsa shi ne ceto jihar Gombe daga abin da ya bayyana a matsayin mulkin masu harkar kasuwanci.

“Ina tabbatar muku da cewa, kamar yadda kuka sani, ana samun gagarumar tafiya a faɗin ƙasar nan, wadda muka ba wa suna ‘Salon Tafiya’.

“Muna aiki a kan wannan tafiya tare da shugabanninmu a faɗin ƙasar, ciki har da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, tsofaffin gwamnoni da ministoci.

“Manufar wannan tafiya ita ce ceto ƙasar nan daga halin da take ciki na rashin tsaro, matsin tattalin arziki da ƙarancin ababen more rayuwa,” in ji shi.

Jibrin Dan Barde ya ƙara da cewa, “Yana da muhimmanci mu dawo gida domin sabunta rajistar membobimmu kuma mun kuduri aniyar ci gaba da wannan tafiya, kuma yanzu ne lokacin da ya dace mu sake sabunta membobimmu.”

Dangane da haɗin kai, ya ce hadakar ta himmatu matuƙa wajen ceto jihar, yana nuna damuwa kan lalacewar ababen more rayuwa da kuma ƙaruwar rashin tsaro.

“Kamar yadda kuke gani, akwai ƙarancin ababen more rayuwa da kuma rashin tsaro, sannan wannan shine iri rashin ɗaukar alhaki ne muke son yaƙi a jihar nan.

“Muna son samar da shugabanci mai ma’ana, mu bai wa kowa damar cin nasara, mu inganta ilimi ba ilimin da mutum ɗaya ko ƙungiya ke sarrafawa kamar kamfani mai iyaka ba,” in ji shi.

Da yake bayyana dalilin komawa ADC, Dan Barde ya ce jam’iyyar na wakiltar sabon zamani, tare da kira ga wasu da su shigo cikinta.

“Abin da muke son yi yanzu shi ne sabunta membobimmu a ƙarƙashin sabon zamani, kuma ga waɗanda ba mambobi ba, muna kiran su da su shigo ADC domin mu tunkari wannan gwamnati mai ɗaukar alhaki,” in ji shi.

Haka kuma ya gargaɗi al’umma da kada su sayar da ƙuri’un su.

“Kada ku karɓi taliya ko Naira 500 ku sayar da ƙuri’unku yace waɗannan darussa ne masu muhimmanci da ya kamata mu koya

Siyasa

Post navigation

Previous Post: FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca
Next Post: Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba

Karin Labarai Masu Alaka

Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar Ya Shiga Jam’iyyar APC Siyasa
Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura Labarai
Kauran Gwandu Zai Inganta Wutan Lantarki A Kebbi Siyasa
Gwamnatin Tarayya Na Kokarin Hana Demokraɗiyya A Najeriya Siyasa

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shari’ar Abubakar Malami Ta Kaura Zuwa Sabon Alkali Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Duniyar Dambe A Makon Jiya Nishadi
  • Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen Afrika
  • Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
  • Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
  • Jami’an Tsaron Pakistan Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Labarai
  • Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa Labarai
  • Ko Arsenal Zata Iya Lashe Gasar Firimiya lig Na Bana Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.