Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
Published: May 18, 2026 at 10:21 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: May 18, 2026

Kotu ta bayar da belin Nasir El-Rufai kan Naira miliyan 100

Wata babbar kotu da ke Abuja a Najeriya bayar da beli ga tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan zargin karan tsaye ga tsaron kasa da ake yi masa.

Mai shari’a Joyce Abdulmalik, yayin yanke hukunci kan buƙatar beli a ranar Litinin, ta gindaya wasu tsauraran sharuɗɗa da El-Rufai zai cika kafin a sake shi.

Kotun ta umarce shi da ya kawo mutum guda da zai tsaya masa beli da adadin kuɗin iri ɗaya.

Kotun ta ce dole ne wanda zai tsaya masa ya kasance mazaunin yankin Maitama ko Asokoro a Abuja, sannan ya ajiye asalin takardar mallakar fili ko gida a ma’ajiyar kotu.

Haka kuma, wanda zai tsaya belin dole ne ya kasance ma’aikacin gwamnatin tarayya mai matsayi bai gaza mataki na 17 ba, tare da gabatar da shaidar biyan albashi na akalla watanni uku, wanda manajan bankinsa a yankin kotun ya tabbatar.

Kotun ta kuma umurci wanda zai tsaya masa ya rantse da takardar bayyana kadarori, ya sanya hannu kan yarjejeniyar beli tare da gabatar da sabon hoton fasfo a ma’ajiyar kotu.

A cikin sharuɗɗan belin, an umurci El-Rufai da ya miƙa duk wasu ingantattun fasfo na ƙasashen waje ga kotu.

Kotun ta kuma buƙaci a gabatar da wasiƙar tabbatarwa daga sashen aikin wanda ya tsaya belin, tare da takardar biyan haraji ta watanni shida da suka gabata.

Mai shari’a Abdulmalik ta kuma umurci wanda ake tuhuma da ya riƙa zuwa hedikwatar Hukumar Tsaro ta DSS a kowace Juma’ar ƙarshe ta wata da ƙarfe 10 na safe domin sanya hannu a rajistar halarta har sai an kammala shari’ar.

Alƙaliyar ta yi gargaɗin cewa rashin bin waɗannan sharuɗɗa zai sa a soke belin kai tsaye.

Kotun ta ƙara umurtar El-Rufai da ya gabatar da wasiƙar shaida daga Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Kaduna.

Haka kuma, kotun ta ba da umarnin a gaggauta sauraron shari’ar da gwamnatin Najeriya ta shigar a kansa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
Next Post: Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi

Karin Labarai Masu Alaka

Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutun Sallar Azumi Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Samar Da Wuta Mai Aiki Da Hasken Rana A Jami’ar ADUSTECH Afrika
Shin Ko Ganawar Zelensky Da Macron Zata Haifar Da ‘Da Mai Ido? Labarai
Masar Tayi Yarjejeniyar Makamashi Da Kasashen Norway Da China Labarai
Ana Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa A Djibouti Yau Juma’a Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
  • Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
  • Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC Siyasa
  • Kasar Habasha Da Turkiyya Sun Kulla Yarjejeniyar Makamashi Afrika
  • Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya Wasanni
  • Yaki Ta Sararin Samaniya Ya Cigaba Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Afrika
  • Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa Labarai
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.