Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
Published: May 18, 2026 at 10:21 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: May 18, 2026

Kotu ta bayar da belin Nasir El-Rufai kan Naira miliyan 100

Wata babbar kotu da ke Abuja a Najeriya bayar da beli ga tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan zargin karan tsaye ga tsaron kasa da ake yi masa.

Mai shari’a Joyce Abdulmalik, yayin yanke hukunci kan buƙatar beli a ranar Litinin, ta gindaya wasu tsauraran sharuɗɗa da El-Rufai zai cika kafin a sake shi.

Kotun ta umarce shi da ya kawo mutum guda da zai tsaya masa beli da adadin kuɗin iri ɗaya.

Kotun ta ce dole ne wanda zai tsaya masa ya kasance mazaunin yankin Maitama ko Asokoro a Abuja, sannan ya ajiye asalin takardar mallakar fili ko gida a ma’ajiyar kotu.

Haka kuma, wanda zai tsaya belin dole ne ya kasance ma’aikacin gwamnatin tarayya mai matsayi bai gaza mataki na 17 ba, tare da gabatar da shaidar biyan albashi na akalla watanni uku, wanda manajan bankinsa a yankin kotun ya tabbatar.

Kotun ta kuma umurci wanda zai tsaya masa ya rantse da takardar bayyana kadarori, ya sanya hannu kan yarjejeniyar beli tare da gabatar da sabon hoton fasfo a ma’ajiyar kotu.

A cikin sharuɗɗan belin, an umurci El-Rufai da ya miƙa duk wasu ingantattun fasfo na ƙasashen waje ga kotu.

Kotun ta kuma buƙaci a gabatar da wasiƙar tabbatarwa daga sashen aikin wanda ya tsaya belin, tare da takardar biyan haraji ta watanni shida da suka gabata.

Mai shari’a Abdulmalik ta kuma umurci wanda ake tuhuma da ya riƙa zuwa hedikwatar Hukumar Tsaro ta DSS a kowace Juma’ar ƙarshe ta wata da ƙarfe 10 na safe domin sanya hannu a rajistar halarta har sai an kammala shari’ar.

Alƙaliyar ta yi gargaɗin cewa rashin bin waɗannan sharuɗɗa zai sa a soke belin kai tsaye.

Kotun ta ƙara umurtar El-Rufai da ya gabatar da wasiƙar shaida daga Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Kaduna.

Haka kuma, kotun ta ba da umarnin a gaggauta sauraron shari’ar da gwamnatin Najeriya ta shigar a kansa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
Next Post: Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamna Abba Ya Gana Da Kwankwaso Kamun Ganawarsa Da Tinubu Siyasa
Rikicin Gabas Ta Tsakiya Yanuna Alakar Kasashen Da Najeriya Afrika
Rangadin Ayyukan Tinubu Ya Kai Tawaga Zuwa Kano Northern Bypass Afrika
Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya Afrika
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugaban Makaman Nukiliya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ’Yar Kasuwa Ta Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Hari Da Saurayinta Ya Kai Mata Afrika
  • Ukraine Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Tsarin Cimma Yarjejeniya Sauran Duniya
  • Harin ‘Yan Daba Ya Hallaka Mutane 70 A Kasar Haiti Labarai
  • Kadan Daga Cikin Abubuwan Da Suka Faru A 2025 A Nan Amurka Amurka
  • Amurka Tace Zata Gama Yakin Iran Cikin Makonni Afrika
  • Kaduna: Masana Sun Nemi A Sauya Tsohon Wurin Zubar Da Shara Na Tudun-Ilu Afrika
  • Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya Afrika
  • Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.