Tarzomar da mayakan wucin gadi a Sudan da ake kira RSF a takaice suka yi a birnin al-Fashir, yana dauke dukkan alamomi na “kisan kare dangi,” kamar yadda ministocin wasu kasashen waje a hukumar kula da hakkin Bil’adama na MDD suka fada a cikin wata sanarwa da suka sake ranar Alhamis.
Gungun kasashen sun sunyi itifakin cewa barnar da RSF ta tafka a al Fashir laifukan yaki ne da kuma cin zarafin Bil’adama, da kisan kiyashi, kamar yadda ministocin suka fada a cikin sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Jamus ta rarraba Alhamis din nan.
Gungun kasashen da suke sa ido kan rikicin na Sudan sun hada da Jamus, da Ireland, da Netherlands, da Norway, da kuma Birtaniya, suka ce suna da shirin hada kai domin ganin haka bata sake aukuwa ba.


