Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya Afrika

Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja
Published: December 8, 2025 at 7:24 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mai bada Shawara kan Tsaro ga Shugaban Ƙasa (NSA), Malam Nuhu Ribadu, ya mika dalibai 100 na makarantar St. Mary Catholic School da ke Papiri, karamar hukumar Agwara a jihar Neja, ga gwamnatin jihar bayan ceto su daga hannun masu garkuwa da mutane.

An gudanar da mika su a Minna a ranar Litinin, inda Wing Cdr. Abdullahi Idi Hong ya wakilci Nuhu Ribadu wajen gabatar da su ga gwamnatin jihar.

Hong ya ce ceton ya biyo bayan makonni na tsauraran hare haren hadin gwiwa tsakanin ofishin mai bawa shugaban kasa Shawara ta fannin tsaro, Hukumar DSS, Rundunar Sojin Najeriya da sauran hukumomin tsaro.

Ya bayyana cewa DSS ta taka “muhimmiyar rawa ta zahiri” a aikin da ya tabbatar da dawowar yaran cikin koshin lafiya.

Ya kara da cewa ofishin Nuhu Ribadu ya fara samar da matakan gaggawa na tsaro a yankunan da ke fuskantar barazana, tare da hadin gwiwar gwamnatocin jihohi, shugabannin gargajiya da na addini domin samar da tsarin tsaro mai dorewa.

Hong ya jaddada cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da aiwatar da manufofin da ke nufin tabbatar da tsaro a makarantu domin kare hakkin kowane yaro ya samu ilimi cikin kwanciyar hankali.

Da yake jawabi, Gwamna Umaru Bago ya bayyana wannan rana a matsayin “muhimmiya a tarihin jihar Neja,” inda ya gode wa Shugaba Bola Tinubu bisa tallafin da ya bai wa hukumomin tsaro wajen cimma nasarar dawo da yaran.

Haka kuma ya yi godiya ga ofishin mai bawa shugaban kasa shawara ta fannin tsaro, jami’an tsaro, hukumomi da al’ummar jihar da suka yi addu’o’i a lokacin da yaran ke hannu.

Gwamnan ya bayyana kwarin gwiwa cewa sauran daliban da har yanzu ke hannun masu garkuwa za a kubutar da su ba da jimawa ba.

Ya tabbatar wa iyaye cewa za a mika yaran ga iyalansu bayan cikakken binciken lafiya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida
Next Post: Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot.

Karin Labarai Masu Alaka

Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya
Wani Abu Ya Fashe A Ofishin Jakadancin Amurka Dake Kasar Norway Afrika
Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace Labarai
GOSEMA Ta Horar Da Mambobin LEMCs A Jihar Gombe Afrika
Iran Tayi Allah Wadai Da Kai Hari Cibiyar Pars Afrika
APC Ta Yi Babban Taron Amincewa Da Shugabannin Jam’iyyar Ba Hamayya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
  • Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa Labarai
  • Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Yobe Ta Sake Jaddada Ƙudirin Rage Mutuwar Yara Afrika
  • Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
  • Ana Sa Ran FIFA Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Najeriya Ta Shigar Kan DR Congo Wasanni
  • Domin Inganta Tsaro Najeriya Ta Sayi Jiragen Yaki A Kasar Italiya Tsaro
  • Kotun Tarayya Tabada Belin Nasiru El Rufai Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.