Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja
Published: December 8, 2025 at 7:24 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mai bada Shawara kan Tsaro ga Shugaban Ƙasa (NSA), Malam Nuhu Ribadu, ya mika dalibai 100 na makarantar St. Mary Catholic School da ke Papiri, karamar hukumar Agwara a jihar Neja, ga gwamnatin jihar bayan ceto su daga hannun masu garkuwa da mutane.

An gudanar da mika su a Minna a ranar Litinin, inda Wing Cdr. Abdullahi Idi Hong ya wakilci Nuhu Ribadu wajen gabatar da su ga gwamnatin jihar.

Hong ya ce ceton ya biyo bayan makonni na tsauraran hare haren hadin gwiwa tsakanin ofishin mai bawa shugaban kasa Shawara ta fannin tsaro, Hukumar DSS, Rundunar Sojin Najeriya da sauran hukumomin tsaro.

Ya bayyana cewa DSS ta taka “muhimmiyar rawa ta zahiri” a aikin da ya tabbatar da dawowar yaran cikin koshin lafiya.

Ya kara da cewa ofishin Nuhu Ribadu ya fara samar da matakan gaggawa na tsaro a yankunan da ke fuskantar barazana, tare da hadin gwiwar gwamnatocin jihohi, shugabannin gargajiya da na addini domin samar da tsarin tsaro mai dorewa.

Hong ya jaddada cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da aiwatar da manufofin da ke nufin tabbatar da tsaro a makarantu domin kare hakkin kowane yaro ya samu ilimi cikin kwanciyar hankali.

Da yake jawabi, Gwamna Umaru Bago ya bayyana wannan rana a matsayin “muhimmiya a tarihin jihar Neja,” inda ya gode wa Shugaba Bola Tinubu bisa tallafin da ya bai wa hukumomin tsaro wajen cimma nasarar dawo da yaran.

Haka kuma ya yi godiya ga ofishin mai bawa shugaban kasa shawara ta fannin tsaro, jami’an tsaro, hukumomi da al’ummar jihar da suka yi addu’o’i a lokacin da yaran ke hannu.

Gwamnan ya bayyana kwarin gwiwa cewa sauran daliban da har yanzu ke hannun masu garkuwa za a kubutar da su ba da jimawa ba.

Ya tabbatar wa iyaye cewa za a mika yaran ga iyalansu bayan cikakken binciken lafiya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida
Next Post: Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot.

Karin Labarai Masu Alaka

Tawagar IMF Tana Kasar Kenya Domin Tattauna Bada Lamuni Labarai
Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Yayi Ajalin ‘Yan Ghana 50 Afrika
Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
Dusar Kankara Ta Hana Jirage Tashi A Birnin Paris Labarai
Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
Amurka Zata Aika Jiragen Yaki Biyu Gabas Ta Tsakiya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Kashe Mutane 7 A Unguwar Dorayi Dake Kano Najeriya
  • An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
  • An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash Labarai
  • Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika
  • Wasu Lauyoyi Sunyi Murabus Yayin Gudanar Da Wata Shari’a A Kasar Amurka Amurka
  • An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau Afrika
  • Venezuela Ta Sako Karin Mutanen Da Take Tsare Dasu Labarai
  • Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.