Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta ƙaddamar da wani gangamin yaƙi da daba ta siyasa da kuma ta kafafen sadarwar zamani, a matsayin wani ɓangare na bikin Ranar Matasa ta Duniya ta shekarar 2026.

An gudanar da gangamin ne ƙarƙashin taken “Makomata Ta Fi Dabar Siyasa Da Ta Kafar Intanet Muhimmanci”, da nufin wayar da kan matasa kan illolin tashin hankalin siyasa, daba a lokacin zaɓe, yaɗa labaran ƙarya, kalaman ƙiyayya, cin zarafi ta intanet da kuma amfani da kafafen sadarwa ba bisa ƙa’ida ba.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya ce babu wata manufa ta siyasa ko wani ɗan ƙaramin tallafin kuɗi da ya cancanci matashi ya sadaukar da makomarsa saboda shi.
Ya yi gargadin cewa daba ta siyasa ta jefa matasa cikin tashin hankali da aikata laifuka, yayin da daba ta kafafen intanet ke samar da sabbin hanyoyin yaɗa labaran ƙarya, kalaman ƙiyayya da tunzura jama’a.

CP Chuso ya buƙaci matasa su riƙa yin tunani sosai kafin wallafawa ko sake yaɗa wani saƙo a kafafen sada zumunta, tare da guje wa duk wani yunƙurin amfani da su wajen haifar da rikici.
Ya kuma yi kira da a ƙara haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro, hukumomin gwamnati, sarakunan gargajiya da shugabannin addinai, ƙungiyoyin farar hula, kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin matasa, domin tabbatar da zaman lafiya da kuma siyasa mai tsafta.
Gangamin ya ƙunshi tattaunawa da masu ruwa da tsaki da kuma zaman amsa tambayoyi, inda mahalarta suka samu damar tattauna dalilan da ke haddasa daba ta siyasa da ta kafafen intanet da kuma illolinsu ga al’umma.

A wani ɓangare na bikin, rundunar ta gudanar da tafiya ta motsa jiki daga hedikwatar ’yan sandan jihar Gombe zuwa filin wasa na Pantami, domin ƙarfafa lafiyar jiki, ɗabi’ar aiki, haɗin kai da kyautata alaƙar ’yan sanda da al’umma.
An kuma kammala bikin da shirin dasa itatuwa ƙarƙashin saƙon “Shuka Zaman Lafiya, Gina Najeriya”, domin ƙarfafa kare muhalli, zaman lafiya da kuma sahihiyar gudummawar matasa wajen ci gaban al’umma.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta sake jaddada aniyarta ta ƙarfafa hulɗa da matasa, gudanar da aikin tsaro cikin rigakafi da kuma haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a jihar.
An gudanar da shirye-shiryen ne ƙarƙashin babban taken Ranar Matasa ta Duniya ta 2026, “Yanayi Mabambanta, Burinmu Ɗaya.”


