Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Najeriya (EFCC) ta shigar da ƙara a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja kan shugaban ƙungiyar Miyetti Allah Kautal Hore, Bello Bodejo, bisa zargin badakalar kuɗi da kuma tallafa wa ayyukan ta’addanci.
Rahotanni sun nuna cewa hukumar ta gabatar da tuhume-tuhume guda 12 a kansa, inda ake zarginsa da hannu a wasu mu’amalolin kuɗi da suka kai kimanin dala miliyan 2.53 na Amurka da ake zargin sun samo asali ne daga haramtattun ayyuka.
A cewar takardun tuhumar da aka gabatar wa kotu, EFCC ta ce Bodejo ya karɓi kuɗaɗe daga tsohon Akanta Janar na Jihar Bauchi, Sa’idu Abubakar, ba tare da amfani da hanyoyin banki da dokokin Najeriya suka tanada ba.
Daga cikin zarge-zargen da ake yi masa, akwai karɓar dala 100,000 a watan Janairun 2022 da kuma dala 200,000 daga wani mutum a wani lokaci daban. Haka kuma, ana zarginsa da karɓar dala 980,000 a watan Fabrairun 2024 da kuma dala 500,000 a watan Maris na shekarar 2024, duk a tsabar kuɗi.
Hukumar EFCC ta kuma yi zargin cewa Bodejo ya mallaki wasu kuɗaɗe da ake kyautata zaton sun samo asali ne daga ayyukan da suka saɓa wa doka, lamarin da ya sa aka shigar da ƙarar a kansa.
Ana sa ran kotun za ta sanya ranar fara sauraron shari’ar nan ba da jimawa ba.
Bello Bodejo dai na ci gaba da cin gajiyar haƙƙinsa na kasancewa marar laifi har sai an tabbatar da zarge-zargen da ake yi masa a gaban kotu.


