Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa
Published: December 1, 2025 at 5:12 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 1, 2025

Dr. Usman Isiyaku, mai sharhi akan al’ammuran yau da kullum, shugabanci na gari, ya ayyana wasu kadan daga cikin tsare-tsaren na gwamnatin Tinubu, a kan al’ammurra da suka shafi jagorancin Najeriya.

Inda yake cewa “Bisa ga al’adar gwamnatin Bola Ahmad Tinubu, ba wani abun mamaki bane ko sabon abu, don ya nada Yarbawa, a mafi akasari da mukamai masu girma. Idan aka duba za’a ga cewar tun fara mulkin shi da irin wannan salon ya fara.”

A wasu lokutta kuwa akan ga cewar Arewa tana da girma, don haka idan aka bata wasu tsirarun mukamai sai aga kamar an yi mata wata hikima. Sau da yawa ‘yan Arewa dake tare da gwamnatin ta shi, basu da wani karfi da za su iya gaya mishi gaskiya. Mafi akasari ma ‘yan abi yarima ne a sha kida.

Don kuwa da yawa daga cikin su, ba wai tunanin kasar ne a zukatan su ba, mafi akasari son kansu da nasu ne a zukatansu. Bugu da kari, duk wani abu da za’a gani a wannan gwamnatin, to yana da alaka da gwamnatin da ta gabata, ta Margayi Muhammadu Buhari.

Tsari ne da ba’a la’akari da cancanta wajen zabo wadanda zasu wakilci kasa, ko jama’a. Don haka ba wani abun mamaki bane don anga nadin jakadu na bangaren Yarbawa da basu da kwatankwacin kashi 10 na adadin yawan mutan Arewa, amma suke da jakadu 11 kana aka kai su kasashe manya a duniya.

Inda ita kuma Arewa ta tashi da jakadu 5 daga bangaren Arewa maso yamma, sai 5 daga Arewa maso gabas, kana wasu 5 da ke wakiltar Arewa ta tsakiya. Abun ala’akari a nan shine, yawan mutane da suka fito daga Arewa maso yamma da ke da jihohi 7, sun fi yawan mutane da suka fito daga baki daya Kudu maso Yamma da aka basu jakadu 11.

Haka kuma, wannan gwamnati ce da take la’akari da mutane da suka wahalar mata koda kuwa basu cancanta, da kuma mutane da suka fito daga bangare daya, ko kuwa bangaranci na addini, da na kabilanci, wanda ta haka ne zai ba mutum damar samu wani babban matsayi, ba la’akari da irin gudunmawar da zaka bada ake yi ba.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano
Next Post: Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi”

Karin Labarai Masu Alaka

Motar Kungiyar Kwallon Kafar Bayelsa United Ta Yi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Real Madrid: Ta Kori Xabi Alonso Bayan Rashin Nasara A Wasan Kofin Sfaniya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Chelsea Tayi Kaca-Kaca Da Barcelona A Gasar UCL Wasanni
  • Shugaba Bola Tinubu Ya Saka Hannu A Dokar Zabe Najeriya
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
  • Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas Najeriya
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Jam’iyyar PDP Na Kara Tsunduma Cikin Mawuyacin Hali Shirye-Shirye
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.