Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano
Published: December 1, 2025 at 4:00 PM | By: Mahmud Kwari | Updated: December 1, 2025

Hukumar kare hakkin dan Adam ta Najeriya tace kawancen aiki data kulla da Kotun Sulhu ta jihar Kano (Kano Multi-Door Court) yana haifar da sakamako mai kyau, ta fuskar warware matsalolin danne hakkoki a tsakanin al’uma.

A taron kaddamar da sabbin mambobin majalisar kula da ayyukan Kotun, shugaban Ofishin shiyyar Kano na hukumar Abdullahi Shehu yace, aiki kafa da kafa da Kotun Sulhun ta Kano na taimakawa bangaren sasanta Jama’a da sulhunta su na hukumar, inda a cewar sa, hadin gwiwar ke bada dama su dai-daita mutanen dake takaddama da juna cikin karamin lokaci.

An kafa Kotun Sulhu ta Kano ne tun kimanin shekaru 20 da suka shude, domin sasanta mutanen dake takaddama da juna akan al’amura daban daban, a wani mataki na rage cunkoson kararraki a gaban kotuna da-ma gidajen yari.

Kotun mai hurumin hukunci dai-dai dana babbar kotun jiha (State High Court), na sauraron kararraki ko korafe-korafe da suka shafi Cinikayya, takaddamar Aure, hakkin makwaftaka da sauran batutuwan yau da kullum na rayuwar Jama’a.

Kotun na aiki tare da hukumomin tsaro, musamman hukumar ‘yan sanda da kungiyoyin kare hakkin bil’adama, Malaman addini, shugabanni al’uma da masu rike da sarautu.

Babbar Jojin Kano, mai shari’a Dije Aboki, ta bukaci Jama’a su kara kaimi wajen amfani da damammakin da Koton ke bayarwa na saukaka shari’u da kuma fito da hakki babu bata lokaci.

Cunkoson kararraki a gaban alkalai a Najeriya na cikin manyan kalubalen da ‘yan kasar ke fuskanta wajen samun adalci a kotuna, musamman wadanda ke tsare a gidajen yari na suna dakon a yanke musu hukunci.

 

Labarai

Post navigation

Previous Post: Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi
Next Post: Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa

Karin Labarai Masu Alaka

An Kama Masu Fasa Kaurin Gawayi A Malawi Afrika
Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika
An Gudanar Da Jana’izar ’Yan Jaridan Da Suka Rasu A Jihar Gombe Labarai
Dusar Kankara Ta Hana Jirage Tashi A Birnin Paris Labarai
Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika
Baitul Malin Amurka Zata Bawa Venezuela Da Cuba Damar Sayar Da Mai Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya
  • Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai
  • Dakarun Pakistan Da Afghanistan Sunyi Arrangama Labarai
  • Shugaba Bola Tinubu Ya Saka Hannu A Dokar Zabe Najeriya
  • Jami’an Tsaron Pakistan Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Labarai
  • Wani Bayahude Ya Harbe Bafalatsine Dan Shekaru 16 Tsaro
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
  • Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.