Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano
Published: December 1, 2025 at 4:00 PM | By: Mahmud Kwari | Updated: December 1, 2025

Hukumar kare hakkin dan Adam ta Najeriya tace kawancen aiki data kulla da Kotun Sulhu ta jihar Kano (Kano Multi-Door Court) yana haifar da sakamako mai kyau, ta fuskar warware matsalolin danne hakkoki a tsakanin al’uma.

A taron kaddamar da sabbin mambobin majalisar kula da ayyukan Kotun, shugaban Ofishin shiyyar Kano na hukumar Abdullahi Shehu yace, aiki kafa da kafa da Kotun Sulhun ta Kano na taimakawa bangaren sasanta Jama’a da sulhunta su na hukumar, inda a cewar sa, hadin gwiwar ke bada dama su dai-daita mutanen dake takaddama da juna cikin karamin lokaci.

An kafa Kotun Sulhu ta Kano ne tun kimanin shekaru 20 da suka shude, domin sasanta mutanen dake takaddama da juna akan al’amura daban daban, a wani mataki na rage cunkoson kararraki a gaban kotuna da-ma gidajen yari.

Kotun mai hurumin hukunci dai-dai dana babbar kotun jiha (State High Court), na sauraron kararraki ko korafe-korafe da suka shafi Cinikayya, takaddamar Aure, hakkin makwaftaka da sauran batutuwan yau da kullum na rayuwar Jama’a.

Kotun na aiki tare da hukumomin tsaro, musamman hukumar ‘yan sanda da kungiyoyin kare hakkin bil’adama, Malaman addini, shugabanni al’uma da masu rike da sarautu.

Babbar Jojin Kano, mai shari’a Dije Aboki, ta bukaci Jama’a su kara kaimi wajen amfani da damammakin da Koton ke bayarwa na saukaka shari’u da kuma fito da hakki babu bata lokaci.

Cunkoson kararraki a gaban alkalai a Najeriya na cikin manyan kalubalen da ‘yan kasar ke fuskanta wajen samun adalci a kotuna, musamman wadanda ke tsare a gidajen yari na suna dakon a yanke musu hukunci.

 

Labarai

Post navigation

Previous Post: Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi
Next Post: Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar Zabe A Kasar Honduras Ta Sanar Da Nasry Asfura A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Shugaban Ƙasa Afrika
Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026, Labarai
Rasha Ta Gargadi Amurka Da Isra’ila Kan Harin Iran Afrika
Tattalin Arzikin Kasar Bahrain Ya Bunkasa Sakamakon Ruruwar Masu Yawon Bude Ido Labarai
Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar Labarai
  • Harin Da Israela Ta Kai Gaza Yayi Ajalin Mutane 27 Da Yara Uku Labarai
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
  • Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu Afrika
  • Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.