Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa zai dage kai hari kan cibiyar makamashi ta kasar Iran har zuwa kwanaki 10, kamar yadda fadar gwamnatin Tehran ta bukata, kuma yace tattaunawa da Iran na tafiya yadda ake so, duk da cewa jami’an Iran sun yi watsi da kudurin da aka gabatar na kawo karshen yaki, suna mai cewa akwai bangaranci, kuma babu adalci a ciki.
Yakin yayi sanadiyyar dubbannan rayuka, kuma yayi illa ga tattalin arzikin duniya, inda farashin makamashi ya tashi tun bayan da Amurka da Isra’ila suka farwa Iran da yaki, a ranar 28 ga Watan Fabrairu, bayan an kasa cimma yarjejeniya a tattaunawa kan shirin nukiliya na Iran.
A jiya Alhamis ne, yayin tattaunawa da majalisar ministoci a fadar White House, Trump yayi barazanar karin matsin lamba ga Iran idan bata cimma yarjejeniya ba, kafin daga baya ya wallafa a shafin sada zumunta cewa zai dakata kaiwa cibiyar makamashi ta Iran zuwa kwanaki 10.


