Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu
Published: November 24, 2025 at 11:29 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 25, 2025

Gwamnan Jihar Gombe, ya bayar da umarnin rufe dukkan makarantun jihar daga yanzu zuwa ranar Juma’a, 28 ga Nuwamba, 2025.

Shugaban Hukumar ilimi matakin farko a Jihar Gombe, wato SUBEB, Farfesa Esrom Jocthan Toro, ne ya isar da umarnin gwamnan yayin taro da ya gudanar da dukkan Sakatarorin Ilimi na ƙananan hukumomi a ofishinsa.

Farfesa Esrom ya tabbatar da kudirin Gwamna Inuwa Yahaya na ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a, yana mai cewa umarnin rufe makarantu mataki ne na kariya domin kauce wa duk wani lamari marar dadi.

Ya ce dukkan jarabawa za a gudanar da su tsakanin yau da ranar Juma’a 28, tare da kira ga iyaye da kada su shiga damuwa domin gwamnati na ƙoƙarin tabbatar da tsaro yadda ya kamata.

Shugaban SUBEB ɗin ya kuma umarci dukkan Sakatarorin Ilimi da su tanadi duk bayanan da suka shafi makarantun da ke karkashin su, domin kwamitin farfaɗo da makarantun zai fara zagayawa wasu daga cikin makarantun da aka zaɓa domin tantancewa da nazari, kafin a bayar da shawarwari.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC
Next Post: Wasu Yara 50 Sun Kubuta Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda

Karin Labarai Masu Alaka

Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos Afrika
Hukumar Zabe Ta Saukaka Gudanar Da Rijistar Katin Zabe A Najeriya Labarai
Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasashen Yankin Gulf Sun Bukaci Amurka Takawo Karshen Iran Afrika
  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin Labarai
  • Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
  • Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya Afrika
  • ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji Afrika
  • Kasar Ghana Ta Tono Gold Na Miliyoyin Kudade Kimiya
  • Rundunar Sojin Amurka Zasu Kaiwa Iran Hari Amurka
  • Allah Ya Yi Wa Sheikh Dahiru Bauchi Rasuwa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.