Shugaban Amurka Donald Trump ranar Litinin ya gargadi Iran cewa Amurka zata goyi bayan wani gagarumin farmaki kan kasar mudddin ta ci gaba da aikin kera makamai masu linzami, da kuma Nukiliya.
Mr. Trump ya kuma ja kunnen Hamas cewa zata fuskanci mawuyacin hali muddin bata amince ta kwance damara ba.
Da yake magana a wani taro da manema labarai tare da PM Isra’ila Benjamin Netanyahu, bayan ganawa da suka yi a wurin shakatawarsa da ake kira Mar-a-Largo a Florida, Trump yace yana samun bayanai cewa Iran tana aikin sake farfado da makamanta, bayan gagarumin harin da Amurka ta kai mata cikin watan Yunin bana.
Trump wadda a baya bayan nan ya kawo batun cimma yarjejeniya da Iran kan shirin Nukiliyarta, ya fadawa manema labarai cewa ganawarsa da Netanyahu ta maida hankali ne wajen ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya a Gaza wacce take tangal tangal da shike gaba aka kulla, da kuma damuwar da Isra’ila take dashi game da Iran, da kuma Hezbollah a Lebanon.
Iran wacce ta kara da Isra’ila na tsawon kwanaki 12, ta fada makon jiya cewa tayi gwajin makamai masu linzmi har sau biyu cikin wannan wata.


