Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Isra’ila Ta Dau Alwashin Kawo Karshen Falasdi
Published: November 17, 2025 at 4:02 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Firay ministan bani Isra’ila Benjamin Netanyahu, ya lashi takobin yin adawa da duk wani yunkurin kafa kasar Falasdinu, yana mai cewa yin hakan kamar tukuici ne ga kungiyar Hamas.

A yau Litinin ne Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya yake shirin jefa kuri’a a kan wani kudurin da Amurka ta zana game da Gaza, wanda ya bar kofa a bude ta kafa kasar Falasdinu nan gaba.

Kudurin na Amurka zai nemi iznin MDD na kafa wata rundunar daidaita al’amura a Gaza, duk da adawar da kasashen Rasha da China da wasu na larabawa suke nunawa da yin hakan.

Hamas da wasu kumgiyoyin Falasdinawa ma sun yi gargadi game da kudurin na Amurka a jiya Lahadi, inda suke cewa wannan yunkuri ne na garkama wa zirin Gaza wata runduna mai goyon bayan Isra’ila tare da hana Falasdinawa ikon gudanar da al’amuransu. Kungiyoyin suka ce in dai har za a kafa wannan rundunar, tilas ba zata kunshi Isra’ila ba, kuma tilas ta kasance karkashin ikon MDD kai tsaye.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya
Next Post: Zelensky Na Ukraine Zai Gana Da Takwaransa Na Faransa A Yau

Karin Labarai Masu Alaka

“Yan Wasan Super Eagles Sun Karbi Alkawarin Da Gwamnati Tayi Musu AFCON 2023 Labarai
Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ya Ziyarci Pindiga Labarai
Kasar Gabon Ta Nemi Tallafin Asusun Bada Lamuni Na IMF Afrika
Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace Labarai
‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
Venezuela Ta Sako Karin Mutanen Da Take Tsare Dasu Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Tawayen Kungiyar M23 Sun Tsagaita Sakamakon Rokon Da Amurka Tayi Amurka
  • Gwamnatin Amurka Na Kokarin Watsi Da Tsohuwar Dokar Jones Labarai
  • Za’a Gurfanar Da Sojojin Da Ake Zargi Da Yunkurin Juyin Mulki Najeriya
  • Maganganun Jami’an Shige Da Fice Dana Shugaban Kasa Trump Suna Cin Karo Da Juna Amurka
  • An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
  • Kakakin Majalisar Kasar Amurka Yana Tsaka Mai Wuya Game Da Kasafin Kudi Amurka
  • Hawan Sallah Daga Masarautar Kaltungo Nishadi
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.