Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika

Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace
Published: December 8, 2025 at 8:03 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya jinjinawa hukumomin tsaro bisa kokarinsu na kubutar da dalibai 100 na makarantar Papiri Catholic School da ke Jihar Neja.

Yayin da ya bayyana farin cikinsa kan dawowar daliban cikin lafiya, Shugaba Tinubu ya kuma umarci hukumomin tsaro da su tabbatar da gaggawar kubutar da sauran dalibai 115 da malamansu da ke hannun masu garkuwa.

Shugaban Kasar ya tabbatar wa iyayen daliban cewa gwamnatin tarayya tare da gwamnatin Jihar Neja na aiki tare domin ganin an dawo da dukkan wadanda aka sace cikin koshin lafiya.

“Ina da cikakken bayani kan dawowar dalibai 100 na makarantar Catholic da ke Jihar Neja.

Ina murnar wannan cigaba tare da Gwamna Umar Bago, kuma ina yabawa hukumomin tsaro bisa jajircewarsu tun bayan mummunan lamarin da ya faru ranar 21 ga Nuwamba.

“Umarni na ga hukumomin tsaro a bayyane yake, dole ne a ceto dukkan daliban da sauran ’yan Najeriya da aka sace, a dawo da su gida lafiya sannan dole mu tabbatar da an ciro kowa ba tare da barin kowa a baya ba.

Gwamnatin tarayya za ta ci gaba da aiki tare da jihar Neja da sauran jihohi domin kara tsaro a makarantun mu da samar da mafi ingancin muhalli na ilmantarwa ga yaranmu.

“Daga yanzu, hukumomin tsaro tare da haɗin gwiwar gwamnoni dole su dakile sake faruwar irin wadannan sace sacen, ya kuma zama wajibi yaranmu su daina zama a wajajen da ’yan ta’adda za su rika kai hari don karya karatunsu da jefa kan su da iyalansu cikin bakin ciki,” in ji Shugaba Tinubu.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot.
Next Post: An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio

Karin Labarai Masu Alaka

Ruwa Kamar Da Bakin Kwarya Ya Haifar Da Mutuwar Mutane A Nairobi Afrika
Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
Shugaban Amurka Yace Sojojin Amurka Dana Iran Sunyi Taho Mugama Amurka
Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina Labarai
Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya Afrika
Kasashen Faransa Da Italiya Sun Nuna Rashin Amincewa Da Matakan Sojoji Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
  • Najeriya Zata Kara Mai Da Take Hakowa Afrika
  • Mayakan Houthi Zasu Shiga Yakin Amurka Da Isra’ila Afrika
  • Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada Afrika
  • Allah Ya Yi Wa Sheikh Dahiru Bauchi Rasuwa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
  • Sojojin Amurka Sun Kutsa Cikin Kasar Iran Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.