Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace
Published: December 8, 2025 at 8:03 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya jinjinawa hukumomin tsaro bisa kokarinsu na kubutar da dalibai 100 na makarantar Papiri Catholic School da ke Jihar Neja.

Yayin da ya bayyana farin cikinsa kan dawowar daliban cikin lafiya, Shugaba Tinubu ya kuma umarci hukumomin tsaro da su tabbatar da gaggawar kubutar da sauran dalibai 115 da malamansu da ke hannun masu garkuwa.

Shugaban Kasar ya tabbatar wa iyayen daliban cewa gwamnatin tarayya tare da gwamnatin Jihar Neja na aiki tare domin ganin an dawo da dukkan wadanda aka sace cikin koshin lafiya.

“Ina da cikakken bayani kan dawowar dalibai 100 na makarantar Catholic da ke Jihar Neja.

Ina murnar wannan cigaba tare da Gwamna Umar Bago, kuma ina yabawa hukumomin tsaro bisa jajircewarsu tun bayan mummunan lamarin da ya faru ranar 21 ga Nuwamba.

“Umarni na ga hukumomin tsaro a bayyane yake, dole ne a ceto dukkan daliban da sauran ’yan Najeriya da aka sace, a dawo da su gida lafiya sannan dole mu tabbatar da an ciro kowa ba tare da barin kowa a baya ba.

Gwamnatin tarayya za ta ci gaba da aiki tare da jihar Neja da sauran jihohi domin kara tsaro a makarantun mu da samar da mafi ingancin muhalli na ilmantarwa ga yaranmu.

“Daga yanzu, hukumomin tsaro tare da haɗin gwiwar gwamnoni dole su dakile sake faruwar irin wadannan sace sacen, ya kuma zama wajibi yaranmu su daina zama a wajajen da ’yan ta’adda za su rika kai hari don karya karatunsu da jefa kan su da iyalansu cikin bakin ciki,” in ji Shugaba Tinubu.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot.
Next Post: An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnonin Arewa Sun Kaddamar da Kwamitin Asusun Tsaro Afrika
Allah Ya Yiwa Shahararren Dan Jarida Saleh Shehu Ashaka Rasuwa Labarai
Haɗin Gwiwar GOSERC Da Savannah Zai Ƙarfafa Rarraba Wutar Lantarki A Faɗin Jihar Gombe Afrika
Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
Kasar China Tana Cigaba Da Nuna Fin Karfi Ga Kasar Taiwan Labarai
An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Tsaurara Tsaro Yayin Da Tehran Ke Shirin Karɓar Masu Jimamin Ayatollah Khamenei Afrika
  • Shugaban Amurka Yace Sojojin Amurka Dana Iran Sunyi Taho Mugama Amurka
  • Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Laraba 11.19.2025 Rediyo
  • Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Samun Sakamako Mai Kyau A Tattaunawa Da Amurka Amurka
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Sake Fasalin Shirin NYSC Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.