Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika

Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot.
Published: December 8, 2025 at 7:30 PM | By: Bala Hassan

Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot,

Dangantakar ta kara Tsamari ne bayan da Kocin Liverpool, Arne Slot ya cire jeren sunayen tawagar da za ta fafata da Inter Milan, ba tare da Salah ba, bayan dan wasan dan Ƙasar Masar yayi wasu kalamai masu tayar da hankali a kwanaki da suka haifar da rikici a Anfield.

An cire fitaccen dan wasan Liverpool Mohamed Salah daga tawagar da za ta fafata da Inter Milan a gasar zakarun Turai wadda hakan ya tada sabon rikici da kocin Arne Slot.

Tsohon dan wasan a Anfield, wanda ya taka rawar gani wajan samun nasarar Liverpool a gasar Premier a kakar wasa ta bara a karkashin Slot, yanzu yana fuskantar makoma mara tabbas a kulob din hakan na kara ruruwa wutan rikici a bayan fage.

Majiyoyin da ke kusa da ƙungiyar sun bayyana cewa rikicin da ya ɓarke ​​tsakanin Salah da Slot ya wargaza dangantakar da ta daɗe tana tsakanin ɗan wasa da koci bayan wani rahoto daga Fabrizio Romano cewa za a iya cire ɗan wasan na Masar.

Hakan ta biyo bayan maganar da Salah ya yi bayan da aka ajiye shi a benci  karo na uku a jere ciki harda wasan da Liverpool tayi da Leeds United, inda kalaman bai yi wa Slot daɗi ba, wanda hakan ya haifar da rashin jituwa da masu sharhi suka bayyana a matsayin “wanda ba zai iya gyaruwa ba.”

Wannan rashin jituwa ya yi tsanani har aka cire Salah daga tawagar Liverpool da za ta je Italiya don fafatawa da Inter Milan UCL, wanda hakan ke nuna sako a bayyane daga shugabannin ƙungiyar.

Duk da Salah ya atisaye da ‘yan uwansa, magoya bayan Liverpool suna mamakin wannan mataki, ganin yadda Salah ya kasance ɗaya daga cikin manyan ‘yan wasan ƙungiyar da kuma muhimmiyar rawar da ya taka a kakar wasansu ta Zakarun Turai.

Rashin ɗan wasan gaban na Masar ya haifar da manyan tambayoyi game da alkiblar ƙungiyar da kuma yadda suke shirin durkusar da hazakarsa a gaba.

Yayin da wannan labarin ke ci gaba da bayyana, magoya bayan Liverpool suna jira don sanin ko tauraron dan wasansu zai iya murmurewa daga wannan rikicin.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja
Next Post: Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace

Karin Labarai Masu Alaka

Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
CAF Ta Ci Tarar Ƙasar Masar Dala 5,000 AFCON 2025 Wasanni
Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025 Wasanni
Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika
Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sojojin Isra’ila Sun Kashe Babban Kwamandan Kungiyar Hezbollah Afrika
  • Mutane Da Dama Sun Rasa Rayukansu Yayin Rikici A Uganda Siyasa
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi Afrika
  • Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya
  • Sakataren Gwamnatin Amurka Ya Bayyana Bawa Kungiyoyin Agaji Damar Kai Taimako Sudan Amurka
  • Amurka Zata Bada Gudunwa Ga Masu Zanga-Zanga A Iran Sauran Duniya
  • An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
  • Wasan Dambe Ya Dau Sabon Salo A Jihar Inugu Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.