Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot.
Published: December 8, 2025 at 7:30 PM | By: Bala Hassan

Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot,

Dangantakar ta kara Tsamari ne bayan da Kocin Liverpool, Arne Slot ya cire jeren sunayen tawagar da za ta fafata da Inter Milan, ba tare da Salah ba, bayan dan wasan dan Ƙasar Masar yayi wasu kalamai masu tayar da hankali a kwanaki da suka haifar da rikici a Anfield.

An cire fitaccen dan wasan Liverpool Mohamed Salah daga tawagar da za ta fafata da Inter Milan a gasar zakarun Turai wadda hakan ya tada sabon rikici da kocin Arne Slot.

Tsohon dan wasan a Anfield, wanda ya taka rawar gani wajan samun nasarar Liverpool a gasar Premier a kakar wasa ta bara a karkashin Slot, yanzu yana fuskantar makoma mara tabbas a kulob din hakan na kara ruruwa wutan rikici a bayan fage.

Majiyoyin da ke kusa da ƙungiyar sun bayyana cewa rikicin da ya ɓarke ​​tsakanin Salah da Slot ya wargaza dangantakar da ta daɗe tana tsakanin ɗan wasa da koci bayan wani rahoto daga Fabrizio Romano cewa za a iya cire ɗan wasan na Masar.

Hakan ta biyo bayan maganar da Salah ya yi bayan da aka ajiye shi a benci  karo na uku a jere ciki harda wasan da Liverpool tayi da Leeds United, inda kalaman bai yi wa Slot daɗi ba, wanda hakan ya haifar da rashin jituwa da masu sharhi suka bayyana a matsayin “wanda ba zai iya gyaruwa ba.”

Wannan rashin jituwa ya yi tsanani har aka cire Salah daga tawagar Liverpool da za ta je Italiya don fafatawa da Inter Milan UCL, wanda hakan ke nuna sako a bayyane daga shugabannin ƙungiyar.

Duk da Salah ya atisaye da ‘yan uwansa, magoya bayan Liverpool suna mamakin wannan mataki, ganin yadda Salah ya kasance ɗaya daga cikin manyan ‘yan wasan ƙungiyar da kuma muhimmiyar rawar da ya taka a kakar wasansu ta Zakarun Turai.

Rashin ɗan wasan gaban na Masar ya haifar da manyan tambayoyi game da alkiblar ƙungiyar da kuma yadda suke shirin durkusar da hazakarsa a gaba.

Yayin da wannan labarin ke ci gaba da bayyana, magoya bayan Liverpool suna jira don sanin ko tauraron dan wasansu zai iya murmurewa daga wannan rikicin.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja
Next Post: Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace

Karin Labarai Masu Alaka

CAF, Zata Ci Tarar Wasu Kasashe AFCON 2025 Wasanni
Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Senegal Yaki Amincewa Da Hukuncin CFA Afrika
CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya Wasanni
Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland Wasanni
FIFA Na Shirin Fadada Babban Na’urar VAR A Gasar Cin Kofin Duniya 2026. Wasanni
Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani Najeriya
  • An Kashe Sojojin Ukraine Dubu 55 A Kasar Rasha Afrika
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
  • NDLEA Ta Kama Dan Kasuwa Da Ke Yunkurin Safarar Hodar Iblis Afrika
  • Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe Afrika
  • Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
  • Newcastle Na Dab Da Kammala Yarjejeniyar Daukar Højbjerg Daga Marseille Kan €15m Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.