Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Senegal Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirka Afcon 2025.
Published: January 19, 2026 at 6:51 AM | By: Bala Hassan

Senegal ta lashe gasar cin kofin kasashen nahiyar afirka Afcon na shekarar 2025.

A ranar Lahadi 18/01/2026 an fafata a wasan karshe na gasar cin kofin kwallon kafa ta kasashen Afirka wadda ya guda a Kasar Moroko.

Senegal ce ta lashe gasar akan masu masaukin baki kasar Moroko da ci 1-0 bayan da akwa kwashe mintoci 120, ana fafatawa.

Pape Gueye ne ya jifa kwallo daya tilo da ta ba Senegal nasara a cikin mintuna na 94, cikin karin lokaci na minti 15 din farko (Extra time).

A lokacin da ake cikin wasan Senegal ta fice daga filin wasa saboda rashin amincewa da bugun daga kai sai maitsaron raga da aka ba wa Moroko a ƙarshen mintuna 90 din farko bayan da da alkalin wasa ya duba na’ura mataimakawa alkalin wasa na VAR an kwashe tsawon minti 14 kafin daga bisani Senegal ta dawo, aka buga sai dai Ibrahim Diaz, ya zubar da fenaretin bayan da mai tsaron ragar Senegal Mendy ya cafke da hannunsa.

An bada manyan kyautuktuka guda uku Brahim Diaz dan wasan Moroko ya lashe kyautar wadda ya fi zura ƙwallo a gasar ta Afcon.

Sai mai tsaron ragar Moroko Yassine Bounou, shi ne mai tsaron raga mafi hazaka.

Dan wasan Senegal Sadio Mane shi ne ɗan wasa mafi kwazo a gasar afcon ta bana.

Shugaban hukumar wasan kwallon kafa ta Duniya Fifa Gianni Infantino ne ya miƙa kofin na Afcon wa Sadio Mane.

Kalidou Koulibaly ne kyaftin din Senegal sai dai bai buga wasan karshen ba saboda an dakatar da shi, amma ya zo wurin mika kofi sanye da kayan wasan Senegal.

Yayin da ‘yan wasan Senegal suke murnan lashe gasar sukuwa wasu da cikin yan wasan Moroko an hangosu suna ta sharban kuka ne bayan tashi a wasan.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: ADC Ta Sha Damarar Gwabzawa Da APC A Zaben 2027
Next Post: Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain

Karin Labarai Masu Alaka

AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
Messi Da Cristiano Suna Da Tasiri A Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Wasanni
Wikki Tourist FC: Ta Sallami ‘Yan Wasa Hudu Wasanni
CAF Ta Ci Tarar Ƙasar Masar Dala 5,000 AFCON 2025 Wasanni
Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
Abun Da Kuke Buƙatar Sani Game Da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka 2025 Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Maka Wasu Jami’an Immigration A Kotu Bisa Zargin Rashin Da’a A Birtaniya Labarai
  • Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
  • Hadakar Gwamnatin Najeriya Da Amurka Ne Suka Kai Hari Sokoto Najeriya
  • Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya Kiwon Lafiya
  • Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
  • Jam’iyyar ADC Ta Karbi Peter Obi Da Wasu Manyan ‘Yan-Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.