Jam’iyyar APC a jihar Yobe ta bayyana Alhaji Baba Malam a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani na gwamna na jam’iyyar bayan samun rinjayen kuri’u a zaben da aka gudanar domin fitar da dan takarar jam’iyyar a zaben shekarar 2027.
Sakamakon zaben da aka sanar a zauren tattara kuri’u da ke Damaturu, babban birnin jihar, ya nuna cewa Alhaji Baba Malam ya samu kuri’u 236,711, inda ya doke sauran masu neman takarar da tazara mai yawa.
Dan takara na biyu, Dr. Abubakar Kagu, ya samu kuri’u 9,748, yayin da Bashir Machina ya zo na uku da kuri’u 1,984.
Sauran ‘yan takarar sun hada da Alhaji Hamidu wanda ya samu kuri’u 1,722, sai Modu Ma’aji da ya samu kuri’u 1,371, Mustapha Maihaja mai kuri’u 1,178, da kuma Inusa Mohammed wanda ya samu kuri’u 1,148.
Sanar da sakamakon ya gudana ne a gaban jami’an jam’iyyar, wakilan ‘yan takara da sauran magoya baya da suka hallara domin sauraron yadda zaben ya kaya.
Nasarar da Alhaji Baba Malam ya samu na nuni da irin goyon bayan da yake da shi a cikin jam’iyyar APC a jihar Yobe, yayin da ake sa ran zai jagoranci jam’iyyar a babban zaben gwamna na shekarar 2027.


