Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka
Published: December 27, 2025 at 10:23 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban ƙasar Najeriya Bola Tinubu ya bayyana cewa gwamnatin kasar ta sayi odar jiragen yaƙi guda huɗu daga Amurka, waɗanda za su iso Najeriya nan ba da jimawa ba, domin ƙara ƙarfafa yaƙi da rashin tsaro da ta’addanci.

Tinubu ya bayyana hakan ne a yayin ganawarsa da tawagar kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) a gidansa da ke Lagos.

Ya ce duk da jinkirin isowar jiragen, gwamnati na ci gaba da neman taimako daga ƙasashen waje, ciki har da Turkiyya.

Wannan na zuwa ne bayan Amurka ta kai hare-haren sama kan ‘yan ta’adda a Arewa maso yammacin Najeriya, lamarin da gwamnatin Najeriya ta tabbatar, tana mai cewa an yi shi ne bisa haɗin gwiwar tsaro tsakanin ƙasashen biyu.

Shugaban ƙasar ya kuma tabbatar da cewa shirin kafa ‘yan sandan al’umma da na jiha zai zama gaskiya da zarar majalisar dokoki ta Kasa ta kammala gyare-gyaren dokokin da suka dace.

Tinubu ya jaddada cewa gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen dawo da zaman lafiya da bunƙasar tattalin arziki a ƙasar, duk da ƙalubalen tsaro da ake fuskanta.

Amurka, Najeriya

Post navigation

Previous Post: CAF Ta Ci Tarar Ƙasar Masar Dala 5,000 AFCON 2025
Next Post: Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya Da Poland Za Su Hada Kai Kan Tsaro da Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
Iran Ta Harbo Jiragen Yakin Amurka Biyu Amurka
Shugaban Amurka Zai Sake Gine Gaza Amurka
Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika
Shugaban Trump: Washington Zatayi Cinikayya Da Indiya Amurka
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tura Sojoji Ga Masu Zanga Zanga Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yanayin Yunwa Yana Kara Ta’azarra A Somaliya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Kashe Falatsinawa Biyar A Wani Hari Da Isra’ila Takai Wata Makaranta A Gaza Tsaro
  • Isra’ila Ta Kashe Babban Jami’in Tsaron Iran Ali Larjani Afrika
  • Amurka Da Tarayyar Turai Sun Fidda Sanarwa Afrika
  • Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Zata Binciki Kasar Iran Afrika
  • Amurka Ta Kakaba Takunkumi Ga Kwamandojin Yakin Kasar Sudan Sauran Duniya
  • An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
  • An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.