Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya Afrika

Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe
Published: December 27, 2025 at 1:10 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 27, 2025

Mummunan hatsari yayi Ajalin Mutane bakwai a jihar Gombe, yayinda Gwamna Inuwa Yahaya Ya Miƙa Ta’aziyya Ga Al’ummar Lawanti Sakamakon Wannan Hatsari

Rahotanni sun ce waɗanda abin ya shafa suna kan hanyarsu ta zuwa Maiduguri babban birnin jihar Borno, don halartar wani bikin aure.

An bayyana sunayen mamatan kamar haka, Gambo Abbo, mai shekara 35, Umalkhairi, mai shekara 18, Rabiu Abubakar, mai shekara 28, Fatuma Hassan, mai shekara 28, Amal Abubakar, mai shekara 3 Adamu Bello, mai shekara 4 da Zarau Alhaji, mai shekara 27.

Da yake tsokaci kan wannan mummunan labari, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana lamarin a matsayin babban rashi mai raɗaɗi da ban tsoro, ba kawai ga iyalan da abin ya shafa ba, har ma ga dukkan al’ummar Lawanti, Ƙaramar Hukumar Akko da kuma jihar Gombe baki ɗaya.

Yace mutuwar kwatsam ta irin waɗannan mutane masu tasiri ta taɓa zuƙatan kowa, yana mai cewa babu wata kalma da za ta iya ta’azantar da iyalan waɗanda suka rasa ƙaunatattunsu a cikin irin wannan yanayi mai ban tausayi.

Gwamnan ya jajantawa iyalan waɗanda abin ya shafa, musamman Hakimin Jalingo, Bello Hassan Babangida wanda ya rasa ‘yar uwarsa da kuma yayansa da Idris Lawanti Maigari, wanda ya rasa ‘yarsa da Kansila mai wakiltar Gundumar Akko, Idris A. Isah Lawanti, wanda shi ma ya rasa ‘yan uwa na kurkusa.

Ya yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki ya baiwa iyalan da suka rasu, da ƴan uwa da kuma duk al’ummar Lawanti yayi fatan su zamo masu juriya, haƙuri da ƙarfin halin ɗaukar wannan babban rashi, sannan kuma Allah Ya jiƙan waɗanda suka rasu da rahamarsa.

Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma yi addu’ar Allah ya gafartawa mamatan abyafe kurakuransu, ya karɓi kyawawan ayyukansu ya kuma saka musu da Aljannatul Firdausi.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka
Next Post: Gwamnatin Najeriya Ta Horar Da Matasa Sama 7,000 A Matsayin Masu Tsaron Daji

Karin Labarai Masu Alaka

Sanata Goje: Sakamakon Zaben Daga Abuja Zai Fito Afrika
Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
Haryanzu Abubakar Malami Da Dansa Suna Hannun Hukumar EFCC Labarai
Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya Afrika
Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato Afrika
Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Farfesa Inuwa Ja’afaru Yakarbi Ragamar Shugabancin Jami’ar Kashere Labarai
  • An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa Afrika
  • Wasu Lauyoyi Sunyi Murabus Yayin Gudanar Da Wata Shari’a A Kasar Amurka Amurka
  • An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
  • Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki Najeriya
  • Thailand Da Cambodia Sun Fara Tattauunawa Kan Batun Tsagaita Wuta Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.