Rundunar ‘Yan Sandan jihar Gombe ta gudanar da wani taron gaggawa kan harkokin tsaro tare da shugabannin jam’iyyun siyasa da wakilan Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), domin tattauna yadda za a tabbatar da zaman lafiya gabanin babban zaɓen shekarar 2027.
An gudanar da taron ne a babban ɗakin taro na Rundunar, sakamakon ƙarin damuwa kan yawaitar laifukan da ke da alaƙa da siyasa, musamman amfani da ‘yan daba wajen tayar da tarzoma, yayin da harkokin siyasa ke ƙara ɗaukar zafi kafin lokacin yaƙin neman zaɓe.
Da yake maraba da mahalarta taron, Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya ce an kira taron ne bayan bayanan sirri sun nuna alamun ƙaruwa a ayyukan tashin hankali masu nasaba da siyasa tun kafin fara yaƙin neman zaɓe a hukumance.
Ya bayyana cewa matsalar Kalare da ake fuskanta a jihar, tare da nauyin da ya rataya a wuyan Rundunar na kare rayuka da dukiyoyin al’umma, sun sa ya zama dole a haɗa masu ruwa da tsaki domin nemo mafita.
Kwamishinan ya buƙaci mahalarta taron su bayar da shawarwari masu amfani domin tabbatar da zaman lafiya, yana mai jaddada cewa lokaci mafi dacewa na dakile rashin tsaro shi ne kafin ya rikide ya gagari shawo kansa.
Shi ma da yake jawabi, Daraktan Hukumar Tsaro ta DSS a jihar Gombe, Haruna Nuhu, tare da Kwamandan Hukumar Tsaro da Kare Fararen Hula (NSCDC), sun bayyana taron a matsayin abin a yaba da shi kuma mai matuƙar muhimmanci.
Sun ce irin wannan zama zai ƙara bai wa hukumomin tsaro damar sa ido kan harkokin siyasa tare da tabbatar da bin dokokin zaɓe, suna mai cewa, “Idan za a yi wasan siyasa, dole ne a yi shi bisa ƙa’idoji da dokokin da aka tanada.”
A nata jawabin, Shugabar Sashen Wayar da Kan Masu Zaɓe ta INEC a Jihar Gombe, Misis Rifqatu Maxwell, ta bayyana cewa har yanzu Hukumar ba ta amince da fara yaƙin neman zaɓe ba.
Ta sanar da cewa yaƙin neman zaɓen Shugaban Ƙasa da na Majalisar Dokoki ta Ƙasa zai fara ne a ranar 19 ga Agustan 2026, yayin da na Gwamna zai fara a ranar 9 ga Satumban 2026.
Ta yi kira ga jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu da su bi ƙa’idojin INEC ba tare da karya doka ba, tana mai gargaɗin cewa duk wanda ya saɓa zai fuskanci hukuncin doka.
Shugabannin jam’iyyun siyasa da suka halarci taron sun yi alƙawarin aiwatar da matsayar da aka cimma domin tabbatar da gudanar da siyasa cikin lumana.
Daga cikin waɗanda suka gabatar da jawabai akwai Manjo Janar A. K. Kwaskebe, Adamu H. Garba, Benjamin Sati, mai ba jam’iyyar PDP shawara kan harkokin shari’a, Lawan Maigoro na Jam’iyyar Labour Party da Bobo Benson Abubakar na Jam’iyyar Action Alliance.
Masu jawabin sun kuma buƙaci a magance tushen rikice-rikicen zaɓe, ciki har da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi, zargin nuna son kai wajen aiwatar da dokokin zaɓe da kuma tabbatar da hukunta masu aikata laifukan zaɓe.
A nasa gudunmawar, wani Wakilin kafar yada labarai ya nuna damuwa kan ƙaruwar cin zarafi ta kafafen sada zumunta da yaɗa bayanan ƙarya a lokutan siyasa.
Ya buƙaci a ɗauki matakan kariya, ciki har da yin rajistar masu kula da kafafen yaɗa labarai na jam’iyyun siyasa da ‘yan takara a INEC, tare da tsaurara aiwatar da Dokar Laifukan Yanar Gizo (Cybercrimes Act).
A ƙarshen taron, Kwamishinan ‘Yan Sandan ya gode wa mahalarta bisa gudunmawar da suka bayar, ya kuma yi bayani kan wasu daga cikin batutuwan da aka taso da su kafin a rufe taron da ɗaukar hoton haɗin gwiwa.


