Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Inuwa Ya Bukaci A Kara Zuba Jari A Ilimin Sana’o’i Domin Samar Wa Matasa Aikin Yi Afrika
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar Bamanga Tukur, Sun Yaba Da Gudunmawarsa Ga Najeriya Afrika
  • Tsohon Shugaban PDP, Bamanga Tukur, Ya Rasu Yana da Shekaru 91 Afrika
  • Filato: Gwamnati Ta Ƙarfafa Matakan Kariya Yayin Sake Buɗe Makarantu Afrika
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika

Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki
Published: March 14, 2026 at 7:13 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jami’ai a Afirka suna gargadin cewa tashin goron zabbi da farashin mai yayi sakamakon yakin Iran, zaiyi kalubale ga manufofin tattalin arziki, kuma zaiyi illa ga a wasu muhiman sassa kamar hakar ma’adinai, wadda hakkan zai dagula farfadowar tattalin arzikin kasashe da suke nahiyar.

Manyan bankuna a birane daga Accra zuwa Luanda suna ta rage kudin ruwa a cikin watannin baya bayan nan ganin yadda ake samun faduwar farashin kayayyaki, da kuma samun daidaito a fannin canjin kudaden ketare, da nufin zaburadda tattalin arzikin su. Da alamun yanzu wadannan matakan za su tsaya.

Babban bankin Uganda ne kadai a nahiyar tun ma gabannin fara yakin ya fara taka-tsan-tsan, yanzu yace zai sake nazarin tasirin manufofin ganin sabon kalubalen.

A ranar Alhamis, babban bankin Angola bai rage ko ya kara kudin ruwan da bankuna suke caji a kasar ba, har aka ji gwamnan babban bankin Manuel Tiago Dias yana cewa, kasadar da tattalin arzikin Kasashen ke fuskanta shine tsawon lokaci da yakin zai dauka, wadda zai shafi jigilar taki da sauran su.

Haka nan ana sa ran cewa wasu manyan bankunan kasashe da suke yankin kama daga Ghana, da Najeriya, da Zambia, da ma Kenya duk za su dakatar da matakan sassauta kudin ruwa da bankunan suke karba.

Afrika, Labarai, Sana'o'i, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Gabannin Harin Amurka Da Isra’ila Iran Farisa Ta Shirya Nata
Next Post: MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan

Karin Labarai Masu Alaka

Akwai Yiwuwar Shugaban Ƙasar Afirka Ta Tsakiya Touadera Yasamu Nasara A Karo Na Uku Afrika
Kasar Sham Ta Sallami Wasu Fararen Hula Labarai
Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye Afrika
Kasar Malawi Ta Kaddamar Da Rigakafin Shan Inna Kiwon Lafiya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Inuwa Ya Bukaci A Kara Zuba Jari A Ilimin Sana’o’i Domin Samar Wa Matasa Aikin Yi
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar Bamanga Tukur, Sun Yaba Da Gudunmawarsa Ga Najeriya
  • Tsohon Shugaban PDP, Bamanga Tukur, Ya Rasu Yana da Shekaru 91
  • Filato: Gwamnati Ta Ƙarfafa Matakan Kariya Yayin Sake Buɗe Makarantu
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati Labarai
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
  • An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu Afrika
  • Rasha: Zamu Ba Gwamnatin Venezuel Gudunmawa Sauran Duniya
  • Inuwa Ya Bukaci A Kara Zuba Jari A Ilimin Sana’o’i Domin Samar Wa Matasa Aikin Yi Afrika
  • Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita Najeriya
  • Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20 Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.