Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika

‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
Published: February 11, 2026 at 9:30 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A lokacin da mazauna garin Doma dake jihar Katsinan Nigeria suka kulla yarjejeniyar sulhu da ‘yan ta’adda a watan Satumbar bara, kowa a kauyen yayi fatan hare-haren ‘yan ta’addar ya zo karshe, kuma manoma zasu samu suyi noma a gonakan su cikin kwanciyar hankali.

Da farko abin ya dore, amma ranar 3 ga wannan watan, ‘yan ta’addan dauke da bindigogi suka far ma kauyen, suna bi gida-gida suna harbe mutane, inda suka hallaka a kalla mutane 21, abinda ya wargaza yarjejeniyar da aka kulla a baya.

Wannan ya sa mutane a wasu kauyukan na Katsina, Kaduna, Sakkwato da Kuma Zamfara da suka kulla irin wannan yarjejeniya da ‘yan ta’adda suke zaman dar-dar na tsoron cewa ana iya kai musu farmaki a ko da yaushe.

A watan da ya wuce ne, ministan tsaron Nigeria Christopher Musa ya gargadi hukumomi a kauyukan da su guji kulla irin wannan yarjejeniya da ‘yan ta’adda, saboda hakan na kawo kalubale ga kokarin da hukumomin kasa ke yi na wanzar da tsaro, da kuma dokar kasa na hana yin tattaunawar sulhu da ‘yan ta’adda.

Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
Next Post: Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030

Karin Labarai Masu Alaka

Isra’ila Ta Zantar Da Hukuncin Kisa Ga Masu Kai Hare Hare Labarai
Ministan Kudin Najeriya: Bamu Samu Kudaden Da Muke Tsammani A Wannan Shekarar Ba Najeriya
Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya
Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya Afrika
Iran Ta Harbo Jiragen Yakin Amurka Biyu Amurka
Sama da mutane dubu 500 ne yanbindiga suka kora daga gidajensu a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Burkina Faso Ta Sako Jami’an Rundunar Sojin Saman Najeriya 11 Da Aka Tsare Tsaro
  • Shugaba Trump Yayi Barazanar Tura Sojoji Ga Masu Zanga Zanga Amurka
  • Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
  • Jirgin Sama Ya Fadi A Kano Labarai
  • Taron Masu Mu’amala Da Kafar Facebook A Kano Afrika
  • Baitul Malin Amurka Zata Bawa Venezuela Da Cuba Damar Sayar Da Mai Amurka
  • Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni
  • Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.