Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade
Published: December 7, 2025 at 4:48 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Wassu ‘yan mata da aka ci zarafinsu ta hanyar yin musu fyade, sun karfafawa gwiwan sauran mata da dukkan wadanda ke fuskantar kuntatawa, su rika fitowa karara suna bayyana matsalarsu ga hukumomi da suak dace, don samun adalci.

A ci gaba da yakin neman kawar da duk wani nau’i na cin zarafi, musamman ma ga mata, a kwanaki goma sha shida da majalisar dinkin duniya ta kebe, kungiyar ‘yan jarida mata, reshen jahar Filato ta gabatar da wassu ‘yan mata biyu ga asibitin kwararru na jahar, don ci gaba da duba lafiyarsu.

Chidimma Augustine wacce aka yi wa fyade, ta kuma sami ciki, da yanzu haka ke wata biyar, tace wanda ya mata fyaden ya ki amincewa, balle ma ya dauki nauyin kaita awu, wanda ya cewarta yace yana bin mahaifinta bashin naira dubu biyar.

Ita ma Justina Dusu wanda tace saurayin ta ne ya mata ciki, bayan ta bayyana masa halin da take ciki, ya rufa tad a bugu da sara da adda har ya fasa mata kwayar ido.

Shugaban kungiyar ‘yan jarida mata, reshen jahar Filato, Madam Grace Akwe Gotip tace kungiyar na bukatar hadin kan al’umma wajen hana cin zarafin mata da taimaka wa wadanda suka fuskanci cin zarafi.

Shima shugaban wata kungiyar matasa dake yaki da cin zarafin al’umma, YIAHVA, Mr Pwakim Jacob Choji, yace tilas sai hukumomi sun aiwatar da dokoki masu tsauri, don kau da cin zarafin al’umma.

Dakta Sa’idu Barnabas, wanda ya karbi ‘yan matan a madadin shugaban asibitin, yace za su yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da ‘yan matan sun sami kulawa mai nagarta.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/CIN-ZARAFIN-MATA.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery
Next Post: Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026

Karin Labarai Masu Alaka

CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda Najeriya
An Gano Wasu Boma Bomai Da Aka Binne A Jihar Neja Najeriya
An Kama Tsohon Jakadan Birtaniya A Amurka Peter Mandelson Amurka
Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Tasakawa Sojin Rwanda Takunkumi Afrika
  • Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
  • Gwamnatin Kano Zata Dauki Mataki Game Da Kisan Dorayi Tsaro
  • Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wakilan Majalisar Dokokin Phillipines Suna Yunkurin Tsige Shugaban Kasar Afrika
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
  • An Hana Yada Rahotannin Siyasa A Kasar Uganda Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.