Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Da Alamu Ronaldo Zai Buga Dukkan Wasanni Da Gasar Kofin Duniya A 2026
Published: November 26, 2025 at 3:23 PM | By: Nafisa Ahmad

Da alamun Cristioano Ronaldo zai buga ma Portugal dukkan wasanninta a gasar cin kofin kwallon kafar duniya ta shekara mai zuwa, duk da jan katin da aka ba shi lokacin da ya buge wani dan wasan Ireland da gwiwar hannu.

A yau Talata hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta wallafa hukumcin dakatar da shi daga wasanni uku da ta yanke, amma ta ce wasa daya dole zai rasa, sauran biyu kuma an dage hukumci a kansu har na tsawon shekara guda domin a ga ko zai sake aikata irin abinda yayi har aka ba shi jan katin.

An dakatar da Ronaldo daga buga wasa guda na tilas a lokacin da kasarsa ta buga da Armeniya ta lashe da ci 9-1, abinda ya tabbatar da gurbinta a gasar cin kofin duniyar da za a yi a nan yankin nahiyar Amurka ta arewa a shekara mai zuwa.

Masu fashin baki da dama sun dauka cewa za a dakatar da Ronaldo daga karin wasa guda, ta yadda za a fara buga gasar cin kofin duniyar ba tare da shi ba.

Wannan shine karo na 6 da Ronaldo zai buga ma Portugal kwallo a gasar cin kofin duniya, abinda babu wani dan wasan da ya taba haka.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Chelsea Tayi Kaca-Kaca Da Barcelona A Gasar UCL
Next Post: Tsohon Shugaban Brazil Bolsanaro Zai Tafi Gidan Yari

Karin Labarai Masu Alaka

Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot. Wasanni
Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya Wasanni
CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya Wasanni
Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika
‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kayan Jinya Da Ayyukan Kiwon Lafiya Suna Barazanar Karewa A Sudan Kiwon Lafiya
  • Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland Amurka
  • Majalisar Dattawan Amurka Ta Amince Da Wata Doka Amurka
  • Mutane 27 Sun Rasa Rayukan Su A Najeriya Afrika
  • Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna Afrika
  • Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
  • Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
  • Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.