Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja
Published: May 10, 2026 at 8:03 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon ministan sadarwa na Najeriya Farfesa Isa Ali Pantami ya yi ƙarin haske kan dalilin da ya sa ya taɓa mayar da akwatin zaɓensa zuwa Abuja daga Gombe.

A hirarsa da gidan talabijin na TVC a yau Lahadi, Pantami wanda ɗaya ne daga cikin masu neman tikitin takarar gwamnan jihar Gombe a zaɓen 2027, ya kuma yi tsokaci kan zargin da ake masa na watsi da lamuran jam’iyyar ta APC na tsawon lokaci.

Pantami ya ce ya maida akwatin zaɓensa zuwa Abuja ne a shekarar 2019 saboda muƙamin da ya riƙe na shugaban hukumar NITDA a lokacin, kuma yana daga cikin masu jagorantar abubuwan da suka shafi bayanan intanet da suke da alaƙa da zaɓen, wanda hakan ya sa ake buƙatar kasancewrasa a birnin tarayyar ƙasar.

Amma ya ce yanzu haka ya maida akwatin zaɓensa jihar Gombe.

A ƴan kwanakin nan dai Pantami ya ɗauki hankalin ƴan Najeriya, tun bayan da jam’iyyarsa ta APC ta amince da miƙa tikitin takarar gwamnan jihar Gombe ga Jamilu Isiyaku Gwamna bisa tsarin masalaha, abin da Farfesan ya yi watsi da shi, inda ya ce zai yaƙi “rashin adalcin da aka yi”.

Da aka tambaye shi game da rashin ba da gudummuwa ga harkokin jam’iyyar APC a lokacin da yake riƙe da muƙamin minista, Pantami ya ce ba haka batun yake ba.

Ya ce ya sha bayar da gudummuwar kuɗi ga jam’iyyar a lokuta daban-daban, inda ya yi iƙirarin cewa ko a kwanan nan ya ba da “gudummuwar naira miliyan 50” a yayin babban taron jam’iyar a Abuja, da kuma wata “miliyan 45” a lokacin sabunta rijistar jam’iyyar ta APC.

Shehin Malamin ya ƙara da cewa, ba a taɓa neman wata gudummuwa daga gareshi ya ƙi yi ba.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi
Next Post: Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya

Karin Labarai Masu Alaka

Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai
Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
Rahoton Leken Asiri Yanuna Cewa Harin Amurka Bazai Samar Da Shugabanci A Iran Ba Afrika
Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi Labarai
Farashin Mai A Kasuwannin Duniya Yayi ƙasa Kadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Isra’ila Tace Bazata Sake Kai Hari Kan Cibiyar Gas Ta Iran Ba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
  • An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara Labarai
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi Labarai
  • Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
  • Shugaban Amurka Donald Trump Yace Amurka Zata Kai Babban Farmaki Iran Afrika
  • Tsohon Jagoran Masu Kishin Kasa A Hungry Ya Amince Da Shan Kaye Labarai
  • Jami’an Tsaro A Jihar Borno Sun Kama ‘Yan Bindiga Labarai
  • Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.