Kasar Afirka ta Kudu tace bata da wani dalili da zata yanke alaka da Iran, a cewar darakta janar na harkokin wajen kasar, bayan da aka ce sabon jakadan Amurka na kasar yace alakar Afirka ta Kudu da Iran zai iya kawo cikas wajen kyakkyawar alakar dake tsakanin kasar da Amurka
A wata tattaunawa da kamfanin dillancin labarai na Reuters, a karshen mako, darakta janar na harkokin wajen Afirka ta Kudu, Zane Dangor, ya kuma yi watsi da wasu bukatun gwamnatin Donald Trump, kamar Janye tuhumar kisan kare dangi da kasar ke yiwa Isra’ila, soke shirin karfafa al’ummar bakar fata, da kuma karban shirin tallafin ‘yan gudun hijira na fararen fata.
A watan Augustan shekara data gabata ne shugaban Amurka Donald Trump ya sanya wa Afirka ta kudu kashi 30 cikin 100 na harajin kayan fito daga kasar, abinda zai iya jawo mutane su rasa ayyukan su, kuma a lokacin da kashi uku na mutanen kasar basu da aikin yi. Sannan kuma alakar kasar da Amurka tayi tsami tun bayan da Trump ya zargi gwamnatin kasar da cin zarafin fararen fata, da ikirarin ana kwacewa manoman su filaye.


