Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba
Published: March 16, 2026 at 8:57 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kasar Afirka ta Kudu tace bata da wani dalili da zata yanke alaka da Iran, a cewar darakta janar na harkokin wajen kasar, bayan da aka ce sabon jakadan Amurka na kasar yace alakar Afirka ta Kudu da Iran zai iya kawo cikas wajen kyakkyawar alakar dake tsakanin kasar da Amurka

A wata tattaunawa da kamfanin dillancin labarai na Reuters, a karshen mako, darakta janar na harkokin wajen Afirka ta Kudu, Zane Dangor, ya kuma yi watsi da wasu bukatun gwamnatin Donald Trump, kamar Janye tuhumar kisan kare dangi da kasar ke yiwa Isra’ila, soke shirin karfafa al’ummar bakar fata, da kuma karban shirin tallafin ‘yan gudun hijira na fararen fata.

A watan Augustan shekara data gabata ne shugaban Amurka Donald Trump ya sanya wa Afirka ta kudu kashi 30 cikin 100 na harajin kayan fito daga kasar, abinda zai iya jawo mutane su rasa ayyukan su, kuma a lokacin da kashi uku na mutanen kasar basu da aikin yi. Sannan kuma alakar kasar da Amurka tayi tsami tun bayan da Trump ya zargi gwamnatin kasar da cin zarafin fararen fata, da ikirarin ana kwacewa manoman su filaye.

Afrika, Amurka, Labarai, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Kenya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kasar Rasha
Next Post: Kasashen Yankin Gulf Sun Bukaci Amurka Takawo Karshen Iran

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
Shugaban Amurka Yayi Barazanar Kulle Wani Dan Jarida Amurka
Wani Abu Ya Fashe A Ofishin Jakadancin Amurka Dake Kasar Norway Afrika
Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund Afrika
Gwamnatin Filato Ta Gurfanar Da Maharan Rukuba A Kotu Afrika
‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
  • Kamfanin Mai Na NNPC Yasamu Gwaggwabar Riba Labarai
  • Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
  • Yakin Rasha Da Ukrain Babban Kalubale Ne Ga Kasashen Turai Labarai
  • Fiye Da Mutane 108 Sun Rasa Rayukansu A Ambaliyar Kenya Afrika
  • Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar Ya Shiga Jam’iyyar APC Siyasa
  • An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
  • Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.