Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Kasashen Yankin Gulf Sun Bukaci Amurka Takawo Karshen Iran
Published: March 17, 2026 at 4:16 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kasashen da suke yankin Gulf da farko ba su goyi bayan Amurka ta kai hari kan Iran ba, amma yanzu suna kira da Amurka kada ta dakatar da yakin, ta yadda zata kyale gwamnatin da take Tehran da zata ci gaba da barazana ga kadarorin mai da tattalin arzikin da suka dogara akan su, kamar yadda kamfanin dilancin labarai na Reuters yaji daga majiyoyi uku a yankin na Gulf.

A lokaci daya kuma,wadannan majiyoyi da kuma jakadun kasashen larabawa da suke aiki a kasashen yammacin duniya 5, sunce Washington tana matsawa kasashe da suke yankin Gulf da su shiga yakin da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran. Kamar yadda uku daga cikin su suka fada, shugaba Trump yana so ya nuna cewa kasashe dake yankin suna goyon bayan yakin, domin hakan zai nuna cewa duniya tana goyon bayan matakin, hakan kuma zai karawa yakin goyo bayan Amurka.

“Akwai tunani a duk fadin yankin Gulf cewa, Iran ta wuce gona da iri kan duk wata kasa dake yankin,” inji Abdulaziz Sager, shugaban wata cibiya mai nazari a Saudiyya, wanda yana sane da irin tunanin gwamnati kan wannan rikici.

“Da farko mun kare su, muka ki goyon bayan yakin,” inji Abdulaziz, “amma da zarar suka fara auna hare haren su akan mu, sun zama makiya. Kuma babu wata hanyar da za’a kalle su.

Ahalinda ake ciki kuma shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana fushinsa kan kasashe da suke yammacin duniya wadanda kawayenta ne, saboda sunyi biris da kiran da yayi na cewa su tura jiragen yaki na ruwa domin su taimaka wajen bude mashigin ruwan Hormuz. Yace Amurka ta tallafa ta kuma kare su, amma ga yanzu yadda suke saka mata. Kasashen Jamus da Japan, da Spain, da Italiya suka ce ba za su tura jiragen su domin tallafawa yakin ahalin yanzu ba.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba
Next Post: An Gargadi Kasar Canada Game Da Tura Sojoji Lebanon

Karin Labarai Masu Alaka

An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa Afrika
An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu Afrika
Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
GOSEMA Ta Horar Da Mambobin LEMCs A Jihar Gombe Afrika
Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki Afrika
Ukraine Ta Mika Wa Amurka Daftarin Yarjejeniya Da Rasha Sauran Duniya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Harkar Zirga Zirgar Jiragen Sama Ya Bunkasa A Kenya Afrika
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino Wasanni
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Amurka Zata Kara Tura Sojoji Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika
  • Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
  • Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.