Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Kasashen Yankin Gulf Sun Bukaci Amurka Takawo Karshen Iran
Published: March 17, 2026 at 4:16 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kasashen da suke yankin Gulf da farko ba su goyi bayan Amurka ta kai hari kan Iran ba, amma yanzu suna kira da Amurka kada ta dakatar da yakin, ta yadda zata kyale gwamnatin da take Tehran da zata ci gaba da barazana ga kadarorin mai da tattalin arzikin da suka dogara akan su, kamar yadda kamfanin dilancin labarai na Reuters yaji daga majiyoyi uku a yankin na Gulf.

A lokaci daya kuma,wadannan majiyoyi da kuma jakadun kasashen larabawa da suke aiki a kasashen yammacin duniya 5, sunce Washington tana matsawa kasashe da suke yankin Gulf da su shiga yakin da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran. Kamar yadda uku daga cikin su suka fada, shugaba Trump yana so ya nuna cewa kasashe dake yankin suna goyon bayan yakin, domin hakan zai nuna cewa duniya tana goyon bayan matakin, hakan kuma zai karawa yakin goyo bayan Amurka.

“Akwai tunani a duk fadin yankin Gulf cewa, Iran ta wuce gona da iri kan duk wata kasa dake yankin,” inji Abdulaziz Sager, shugaban wata cibiya mai nazari a Saudiyya, wanda yana sane da irin tunanin gwamnati kan wannan rikici.

“Da farko mun kare su, muka ki goyon bayan yakin,” inji Abdulaziz, “amma da zarar suka fara auna hare haren su akan mu, sun zama makiya. Kuma babu wata hanyar da za’a kalle su.

Ahalinda ake ciki kuma shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana fushinsa kan kasashe da suke yammacin duniya wadanda kawayenta ne, saboda sunyi biris da kiran da yayi na cewa su tura jiragen yaki na ruwa domin su taimaka wajen bude mashigin ruwan Hormuz. Yace Amurka ta tallafa ta kuma kare su, amma ga yanzu yadda suke saka mata. Kasashen Jamus da Japan, da Spain, da Italiya suka ce ba za su tura jiragen su domin tallafawa yakin ahalin yanzu ba.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba
Next Post: An Gargadi Kasar Canada Game Da Tura Sojoji Lebanon

Karin Labarai Masu Alaka

Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142 Labarai
‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara Afrika
Kamfanonin Jiragen Sama Suna Fama Da Karin Farashin Mai Labarai
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin Afrika
Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Amurka
China Ta Yi Kira Da Kasashen Gabas Ta Tsakiya Su Hada Kai Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Da Haɗin Guiwar Gwamnatin Jihar Zamfara Suna Shirin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Jihar Rumbun Hotuna
  • Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika
  • Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a Amurka
  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin Labarai
  • Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
  • Ana Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa A Djibouti Yau Juma’a Afrika
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Kara Sace Mutane A Jihar Naija! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.