Kasashen Canada, da Faransa, da Jamus, da Italiya, jiya Litinin sukayi kira cewa tilas Isra’ila ta kaucewa “matakin tura sojoji cikin Lebanon,” saboda zai haifarda mummunar sakamako kan zamantakewa, kamar yadda suka fada a cikin wata sanarwa ta hadin guiwa da suka fitar.
An jefa Lebnnon cikin yakin na gabas ta tsakiya ne ranar 2 ga watan Maris, bayan da kungiyar Hezbollah da take samun goyon baya daga Iran ta kaiwa Isra’ila hari.
Kungiyar tace ta dauki matakin ne da nufin daukar fansar kashe shugaban addinin Iran Ayatollahi Ali Khameni, wanda aka kashe a ranar farko na fara yakin da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran.
A martanin da Isr’ila ta dauka ya halaka mutane fiye da 880, ya tilastawa mutane milyan daya barin mullahan su, yayinda mutane dubu dari da talatin suke zaune a sansanoni, kamar yadda hukumomi a Lebanon suka fada. Isra’ila tace wadannan mutane da aka raba da mullahansu a Lebanon, ba za su koma gidajen su ba, har sai ta sami tabbacin al’umarta suna zaune lafiya.


