Jam’iyyar APC ta fitar da ɗan takararta na kujerar Sanatan Gombe ta Tsakiya mai ƙunshe da ƙananan hukumomin Akko da Yamaltu-Deba bayan gudanar da zaɓen fidda gwani cikin lumana tare da halartar dimbin magoya bayan jam’iyyar.
Wakilin GTA Hausa Amurka Ke Magana a jihar Gombe, Aliyu Gerengi daga ya ruwaito cewa, bayan kammala zaɓen, jami’in da ya jagoranci zaɓen, Dr. Habu Dahiru, ya bayyana sakamakon a garin Kumo inda ya ayyana tsohon Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda, Mohammed Ahmadu Jarman Deba, a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

Dr. Habu Dahiru ya ce an tantance masu kaɗa ƙuri’a dubu 53 da 310, inda DCP Mohammed Ahmadu ya samu ƙuri’u dubu 42 da 785, lamarin da ya ba shi nasara a kan Sanata mai ci, Muhammad Danjuma Goje, wanda ya samu ƙuri’u dubu 10 da 425.
Da yake jawabi bayan kammala zaɓen, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Akko, Usman Bello Kumo, ya bayyana zaɓen a matsayin wanda aka gudanar cikin adalci da lumana.
Ya yaba wa masu zaɓe bisa abin da ya kira kyakkyawan zaɓi tare da ƙarfafa musu gwiwa da su ci gaba da nuna irin wannan hali a zaɓukan da za su biyo baya.
Usman Bello Kumo ya kuma yi kira ga al’umma da su mara wa dukkan ‘yan takarar APC baya a babban zaɓe mai zuwa domin ci gaba da ayyukan raya ƙasa masu ɗorewa.
A nasa jawabin karɓar nasara, tsohon DCP Mohammed Ahmadu ya gode wa duk waɗanda suka bayar da gudunmawa wajen samun nasararsa tare da alƙawarin ba zai ba su kunya ba. Haka kuma ya yaba wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya bisa samar da daidaito da ya bai wa kowa dama wajen gudanar da zaɓen fidda gwani cikin nasara a faɗin jihar.



