Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
Published: May 18, 2026 at 7:20 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: May 18, 2026

Jam’iyyar APC ta fitar da ɗan takararta na kujerar Sanatan Gombe ta Tsakiya mai ƙunshe da ƙananan hukumomin Akko da Yamaltu-Deba bayan gudanar da zaɓen fidda gwani cikin lumana tare da halartar dimbin magoya bayan jam’iyyar.

Wakilin GTA Hausa Amurka Ke Magana a jihar Gombe, Aliyu Gerengi daga ya ruwaito cewa, bayan kammala zaɓen, jami’in da ya jagoranci zaɓen, Dr. Habu Dahiru, ya bayyana sakamakon a garin Kumo inda ya ayyana tsohon Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda, Mohammed Ahmadu Jarman Deba, a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

Dr. Habu Dahiru ya ce an tantance masu kaɗa ƙuri’a dubu 53 da 310, inda DCP Mohammed Ahmadu ya samu ƙuri’u dubu 42 da 785, lamarin da ya ba shi nasara a kan Sanata mai ci, Muhammad Danjuma Goje, wanda ya samu ƙuri’u dubu 10 da 425.

Da yake jawabi bayan kammala zaɓen, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Akko, Usman Bello Kumo, ya bayyana zaɓen a matsayin wanda aka gudanar cikin adalci da lumana.

Ya yaba wa masu zaɓe bisa abin da ya kira kyakkyawan zaɓi tare da ƙarfafa musu gwiwa da su ci gaba da nuna irin wannan hali a zaɓukan da za su biyo baya.

Usman Bello Kumo ya kuma yi kira ga al’umma da su mara wa dukkan ‘yan takarar APC baya a babban zaɓe mai zuwa domin ci gaba da ayyukan raya ƙasa masu ɗorewa.

A nasa jawabin karɓar nasara, tsohon DCP Mohammed Ahmadu ya gode wa duk waɗanda suka bayar da gudunmawa wajen samun nasararsa tare da alƙawarin ba zai ba su kunya ba. Haka kuma ya yaba wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya bisa samar da daidaito da ya bai wa kowa dama wajen gudanar da zaɓen fidda gwani cikin nasara a faɗin jihar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
Next Post: Sanata Goje: Sakamakon Zaben Daga Abuja Zai Fito

Karin Labarai Masu Alaka

Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco Afrika
Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
Amurka Zata Saidawa Saudiyya Da Jirgin Yaki Samfurin F35 Labarai
Kasar Afirka Ta Kudu Ta Gayyaci Sabon Jakadan Amurka Afrika
Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari Amurka
Mayakan RSF A Sudan Suna Sace Kananan Yara A Lokacin Yake-Yaken Kasar Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Tasakawa Sojin Rwanda Takunkumi Afrika
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
  • Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
  • Kudaden Shigan Kasar Namibia Ya Bunkasa Saboda Tashin Farashin Gwal Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Zata Fara Gwajin Shan Kwaya Kafun Daukar Aiki Kiwon Lafiya
  • An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe Afrika
  • Allah Ya Yi Wa Sheikh Dahiru Bauchi Rasuwa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.