Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
Published: May 18, 2026 at 7:20 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: May 18, 2026

Jam’iyyar APC ta fitar da ɗan takararta na kujerar Sanatan Gombe ta Tsakiya mai ƙunshe da ƙananan hukumomin Akko da Yamaltu-Deba bayan gudanar da zaɓen fidda gwani cikin lumana tare da halartar dimbin magoya bayan jam’iyyar.

Wakilin GTA Hausa Amurka Ke Magana a jihar Gombe, Aliyu Gerengi daga ya ruwaito cewa, bayan kammala zaɓen, jami’in da ya jagoranci zaɓen, Dr. Habu Dahiru, ya bayyana sakamakon a garin Kumo inda ya ayyana tsohon Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda, Mohammed Ahmadu Jarman Deba, a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

Dr. Habu Dahiru ya ce an tantance masu kaɗa ƙuri’a dubu 53 da 310, inda DCP Mohammed Ahmadu ya samu ƙuri’u dubu 42 da 785, lamarin da ya ba shi nasara a kan Sanata mai ci, Muhammad Danjuma Goje, wanda ya samu ƙuri’u dubu 10 da 425.

Da yake jawabi bayan kammala zaɓen, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Akko, Usman Bello Kumo, ya bayyana zaɓen a matsayin wanda aka gudanar cikin adalci da lumana.

Ya yaba wa masu zaɓe bisa abin da ya kira kyakkyawan zaɓi tare da ƙarfafa musu gwiwa da su ci gaba da nuna irin wannan hali a zaɓukan da za su biyo baya.

Usman Bello Kumo ya kuma yi kira ga al’umma da su mara wa dukkan ‘yan takarar APC baya a babban zaɓe mai zuwa domin ci gaba da ayyukan raya ƙasa masu ɗorewa.

A nasa jawabin karɓar nasara, tsohon DCP Mohammed Ahmadu ya gode wa duk waɗanda suka bayar da gudunmawa wajen samun nasararsa tare da alƙawarin ba zai ba su kunya ba. Haka kuma ya yaba wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya bisa samar da daidaito da ya bai wa kowa dama wajen gudanar da zaɓen fidda gwani cikin nasara a faɗin jihar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
Next Post: Sanata Goje: Sakamakon Zaben Daga Abuja Zai Fito

Karin Labarai Masu Alaka

Rundunar Operation Hadinkai Sunyi Nasara Akan ISWAP Da Boko Haram Najeriya
Ƙungiyar Mata Sunyi Kira Ga Jam’iyar P R P Da Ta Dauki Baheejja A Matsayin Mataimakiyar Gwamnan A Bauchi 2027 Labarai
Isra’ila Takai Hare Hare Birnin Tehran Afrika
Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
Jam’iyar NNPP: Abba Kabir Yusuf Yaci Amanar Mu Siyasa
Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Kashe Sojojin Bangladesh A Kasar Sudan Tsaro
  • Tsofin Ma’aikatan Gwamnati Sunyi Zanga Zanga A Jihar Neja Labarai
  • Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
  • Kannywood: Ali Nuhu Ya Shiga Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Tinubu Afrika
  • Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe Najeriya
  • Afirka Ta Kudu Ta Samu Rigakafin Cutar Boro Afrika
  • Wasan Dambe Ya Dau Sabon Salo A Jihar Inugu Wasanni
  • Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.