Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika

Mayakan RSF A Sudan Suna Sace Kananan Yara A Lokacin Yake-Yaken Kasar
Published: January 30, 2026 at 8:05 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 31, 2026

Wani bincike da kamfanin dillacin labarai na Reutres ya yi, ya bankado cewa Sojojin sa kai a Sudan sun sace yara lokacin da suka kwaci birnin al-Fashir a watan Octoba, da kuma lokacin da suka kai hare-hare a yankin na Darfur tun fara yakin basasar da ake ta gwabzawa tsakanin su da sojin kasar. An ce ma wani sa’in suna kashe iyayen yaran ne kafin su dauke su.

Wadanda abun ya faru a kan idon su sun shaidawa kamfanin dillacin Labarai na Reuters cewa, dakarun tawayen RSF sun fadawa iyayen yaran cewa za’a yi amfani da su ne a matsayin bayi don su yi kiwon dabbobi.

Rigima ta kaure ne tsakanin dakarun na RSF da sojojin Sudan tun watan Aprilun shekara ta 2023, kan wanda ya cancanta ya rike ragamar mulkin kasar msi arzikin albarkatu da yalwar kasar noma da kuma tasoshin jiragen ruwa a gabar da kogin bahar maliya.

Duk da cewa masu rajin kare hakki sun bada rahoton cewa duka bangarorin sun tafka laifukan yaki, ciki har da daukan yara don aiki a wajen daga, ba’a kawo rahoto kan sacewa da bautar da yara da kungiyar RSF da ‘yan kawancen ta ke yi ba.

Mutane 26 da abin ya faru a kan idon su, sun zanta da kamfanin dillacin labarai na Reuters ido da ido ko ta wayar tarho, bayan da suka tsere zuwa garin Tawila da ke arewacin Dafur ko kasar Chad. Sun yi bayanin abubuwan da suka faru, inda aka sace kalla yara 56 da shekarun su ya kama daga wata 2 zuwa shekara 17 tun a shekarar 2023.

Afrika, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kungiyar ISIS Ta Dauki Alhakin Harin Kasar Nijar
Next Post: Tattalin Arzikin Kasar Uganda Zai Bunkasa A Wannan Shekarar

Karin Labarai Masu Alaka

Jirgi Marar Matuka Yayi Luguden Wutan A Abu Dhabi Afrika
Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa Afrika
Ministocin Kasar Asia Zasu Gudanar Da Taro A Kasar Malaysia Tsaro
Sakamakon Yakin Gabas Ta Tsakiya Kowacce Gangar Mai Ta Haura Dala 100 Afrika
Kasar Spain Ta Rufe Sararin Saman Kasar Amurka
An Garkame Wani Babban Soja A Kasar Australiya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Akwai Doka Mai Tsanani Wajen Mallakar Bindiga A Kasashen Yammacin Turai Labarai
  • Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC Najeriya
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi Afrika
  • Gwamna Ahmad Aliyu Na Jihar Sokoto Ya Gabatar Da Kasafin Fiye Da Naira Biliyan 700 Labarai
  • Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Da Haɗin Guiwar Gwamnatin Jihar Zamfara Suna Shirin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Jihar Rumbun Hotuna
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.