Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Mayakan RSF A Sudan Suna Sace Kananan Yara A Lokacin Yake-Yaken Kasar
Published: January 30, 2026 at 8:05 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 31, 2026

Wani bincike da kamfanin dillacin labarai na Reutres ya yi, ya bankado cewa Sojojin sa kai a Sudan sun sace yara lokacin da suka kwaci birnin al-Fashir a watan Octoba, da kuma lokacin da suka kai hare-hare a yankin na Darfur tun fara yakin basasar da ake ta gwabzawa tsakanin su da sojin kasar. An ce ma wani sa’in suna kashe iyayen yaran ne kafin su dauke su.

Wadanda abun ya faru a kan idon su sun shaidawa kamfanin dillacin Labarai na Reuters cewa, dakarun tawayen RSF sun fadawa iyayen yaran cewa za’a yi amfani da su ne a matsayin bayi don su yi kiwon dabbobi.

Rigima ta kaure ne tsakanin dakarun na RSF da sojojin Sudan tun watan Aprilun shekara ta 2023, kan wanda ya cancanta ya rike ragamar mulkin kasar msi arzikin albarkatu da yalwar kasar noma da kuma tasoshin jiragen ruwa a gabar da kogin bahar maliya.

Duk da cewa masu rajin kare hakki sun bada rahoton cewa duka bangarorin sun tafka laifukan yaki, ciki har da daukan yara don aiki a wajen daga, ba’a kawo rahoto kan sacewa da bautar da yara da kungiyar RSF da ‘yan kawancen ta ke yi ba.

Mutane 26 da abin ya faru a kan idon su, sun zanta da kamfanin dillacin labarai na Reuters ido da ido ko ta wayar tarho, bayan da suka tsere zuwa garin Tawila da ke arewacin Dafur ko kasar Chad. Sun yi bayanin abubuwan da suka faru, inda aka sace kalla yara 56 da shekarun su ya kama daga wata 2 zuwa shekara 17 tun a shekarar 2023.

Afrika, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kungiyar ISIS Ta Dauki Alhakin Harin Kasar Nijar
Next Post: Tattalin Arzikin Kasar Uganda Zai Bunkasa A Wannan Shekarar

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Yace Tehran Tana Neman Kulla Alaka Da Washington Amurka
An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya Afrika
Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugaban Makaman Nukiliya Afrika
Amurka Ta Kakaba Takunkumi Ga Kwamandojin Yakin Kasar Sudan Sauran Duniya
Manoma Suna Fuskantar Barazanar Karyewa A Kasar Ghana Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
  • Amurka Zata Bada Gudumawar Kudi Dala Bilyan 10 Ga Ayyukan Kwamitin Wanzar Da Zaman Lafiyan Amurka
  • Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kasashen Afirka Amurka
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Afrika
  • Abu Mafi Daukar Hankali A Wasan Dambe Na Yau Wasanni
  • Sojin Kasar Congo Da ‘Yan Tawaye Sun Kara Shiga Yankin Uvira Labarai
  • Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
  • Rivers: ‘Yan Majalisa 16 Sun Canza Sheka Zuwa APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.