Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Shugaban Hukumar NAHCON Ya Yabawa ‘Yan Jarida
Published: June 1, 2026 at 5:02 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya  wato (NAHCON), Ambasada Isma’il Abba Yusuf, ya yaba wa tawagar ‘yan jaridun Najeriya da ke gudanar da aikin yada labarai a Saudiyya bisa yadda suka gudanar da rahotannin Hajjin shekarar 2026 cikin kwarewa da jajircewa.

Ambasada Yusuf ya bayyana hakan ne a yayin wata ganawa da ‘yan jaridar a Ofishin NAHCON dake birnin Makkah ranar Lahadi, inda ya ce ya gamsu matuka da inganci da kuma sahihancin rahotannin da suka rika aikawa daga wuraren ibadar Hajji.

“Na ga ya dace in gana da ku domin in isar da godiya ta kai tsaye. Hakika na yi matukar farin ciki da irin aikin da kuka yi da kuma yadda kuka nuna kwarewa da jajircewa duk da matsin lambar da ke tattare da aikin,” in ji shi.

Ya ce hukumar na shirin aiwatar da wasu gyare-gyare da sauye-sauye domin kara inganta ayyukan Hajji a nan gaba, tare da samar da yanayi mafi dacewa ga ‘yan jarida domin gudanar da aikinsu cikin sauki.

A cewarsa, duk da karancin albarkatun da hukumar ke da su wajen sakawa masu yada labarai, NAHCON na da cikakken masaniya kan irin wahalhalun da suke fuskanta yayin gudanar da aikinsu.

“Mun san irin hatsarori da wahalhalun da aikin ke tattare da su. Mun san lokutan da kuke yin tafiya mai nisa domin neman labari. Saboda haka muna matukar godiya da irin hakurin da kuka nuna da kuma yadda kuka gudanar da aikinku cikin kwarewa,” inji shi

Shi ma da yake jawabi, Kwamishinan NAHCON mai kula da Ma’aikata, Bincike, Watsa Labarai da Ayyukan Laburare, Farfesa Abubakar Yagawal, ya yabawa ‘yan jaridar bisa irin gudunmawar da suka bayar wajen yada bayanai kan ayyukan Hajjin bana.

Ya ce baya ga rawar da suka taka wajen isar da labarai ga al’umma, sun kuma kasance masu bayar da goyon baya ga hukumar a lokuta daban-daban yayin gudanar da ayyukan Hajji.

“Muna matukar godiya da irin kokarin da kuka yi wajen yada ayyukan Hajji da kuma tafiyar da harkokin aikin Hajjin bana. Yawancin rahotannin da aka fitar a wannan shekara sun kasance masu inganci, saboda haka muna mika godiyarmu gare ku baki daya,” in ji Yagawal.

Ya kara da cewa hadin kai tsakanin NAHCON da kafafen yada labarai na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da sahihan bayanai sun isa ga alhazai da kuma ‘yan Najeriya baki daya.

Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
Next Post: NUT Ta Shiga Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani

Karin Labarai Masu Alaka

CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025 Labarai
Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
An Kashe Mayakan Sakai 67 A Pakistan Sauran Duniya
Hare Hare A Kasar Congo Ya Jikkata Mutane Da Dama Afrika
Musa: “Da Yaddar Allah Zamu Ga Bayan Ta’addanci A Najeriya” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Farashin Gangar Mai Yayi Gagarumar Fadi A Kasashen Duniya Labarai
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai
  • Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Chelsea Tayi Kaca-Kaca Da Barcelona A Gasar UCL Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutu Najeriya
  • Hukumomin Kasar China Suna Goyon Bayan Somaliya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.