Dan wasan gaba na ƙasar Poland Robert Lewandowski ya ce zai kokari don samun zura kwallon na 90 a raga a lokacin da kungiyar White-Reds za ta karbi bakuncin Super Eagles na Najeriya a wasan sada zumunci da za’ayi a Stadion PGE Narodowy da ke Warsaw a wannan Laraba.
Lewandowski ya buga wa kasarsa wasanni 166 in da ya zura kwallaye 89.
In har ya samu nasarar zura kwallo a ragar Najeriya, zai kai ga jimillar 90, wanda hakan zai kara fadada tarihinsa na zama dan wasan da ya fi zura kwallaye a tarihin kwallon kafa na ƙasar Poland hakan ya kusanci kwallaye 100.
Ya fara bugawa Poland wasa a ranar 10 ga Satumba, 2008 shekaru 18 kenan.
Dan wasan mai shekaru 37 zai fara wasan ne bayan ya buga mintuna 45 kacal a wasan karshe da kungiyarsa ta buga da Ukraine, wanda ya kare da rashin nasara da ci 2-0.
Mai horas da ƙungiyar ta Poland Jan Urban ya tabbatar da cewa yana shirin yin wasu canje-canje ga ‘yan wasansa na farko, yana mai bayyana cewa mai tsaron raga na Wolfsburg Kamil Grabara zai maye gurbin Marcin Bułka tsakanin mukamai, yayin da Piotr Zieliński shi ma zai fara wasan.
Za’a fafata a wanne da misalin karfe takwas saura kwata agogon Najeriya Nijar Kamaru da Chadi.


