Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Game Da Matsalar Tsaro A Najeriya
Published: January 10, 2026 at 3:06 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 11, 2026

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana aniyarta ta sake ƙarfafa dakarun tsaron ƙasar, domin tunkarar matsalolin tsaro da ke addabar wasu sassa.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ne ya bayyana hakan a yayin taron addu’o’i na musamman da aka shirya domin dakarun tsaron ƙasa a Babban Masallacin Ƙasa da ke Abuja.

Shettima ya yaba da jajircewa da sadaukarwar da dakarun tsaron ƙasar ke yi, musamman waɗanda suka rasa rayukansu a bakin aiki wajen kare martaba da ikon ƙasar, da kuma rayuka da dukiyoyin al’umma.

Taron addu’o’in ya gudana ne a matsayin wani ɓangare na bukukuwan ranar tunawa da gudunmowar da dakarun tsaron Najeriya ke bai wa ƙasa.

Gwamnatin Tarayya ta ware ranar 15 ga watan Janairu na kowace shekara domin karrama dakarun tsaron ƙasar.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar Kano
Next Post: NAHCON Tafara Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026

Karin Labarai Masu Alaka

Farashin Kasuwar Yawon Bude Ido A Kasuwar Hannayen Jari Ya Fadi Afrika
Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya Amurka
‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayin Shanu Tsaro
NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan Afrika
An Kama Maharan Bom Din Maiduguri Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
  • An Kara Wa’adin Zaman Kurkuku A Senegal Ga Masu Auren Jinsi Afrika
  • ‘Yan Sandan Habasha Sun Kama Dubban Albarusai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Trump Ya Bukaci Kasar Iran Ta Mika Wuya Amurka
  • Indiya Da Brazil Sun Kulla Yarjejeniyar Cinikayya Afrika
  • Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
  • Yakin Rasha Da Ukrain Babban Kalubale Ne Ga Kasashen Turai Labarai
  • ‘Yan Kasar Venuzuela Zasu Fara Komawa Gida Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.