Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Kungiyar ‘Yan Ta’adda Masu Alaka Da ISIS Sun Kashe Mutane A Congo
Published: January 26, 2026 at 8:50 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wasu ‘yan kungiyar ‘yan ta’adda da ke da alaka da kungiyar ISIS a gabashin Congo sun hallaka a kalla mutane 25 a cewar masu rajin kare hakki a lardin Ituri.

Wadanda aka kashe sakamakon harin da kungiyar Allied Democratic Forces, wato IDF ta kai, sun hada da maza 15 da aka kone da ran su a wani gida, da wasu 7 da aka harbe a kauyen Apakulu, a yankin Irumu da ke lardin Ituri. Uku kuma an kashe su ne a yankin gudanar da ayyuka na Walese Vonkutu.

Shugaban kungiyar masu rajin kare hakki, Christophe Muyanderu, yace abun ya faru wajajen karfe 4 na asuba, inda rayuka a kalla 25 suka salwanta. Ya kara da cewa wannan hari na ADF kisan gilla ne karara.

Ba’a ji daga kungiyar ta ADF kan lamarin ba.

Jamhuriyar Demokradiyar Congo dai na yawan samun hare-hare a watannin baya bayan nan daga kungiyoyin ‘yan tawaye da suka hada da ADF kuma kungiyar M23 da kasar Rwanda ke marawa baya.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Za’a Gurfanar Da Sojojin Da Ake Zargi Da Yunkurin Juyin Mulki
Next Post: Sojojin Faransa Sun Karyata Zargin Bobi Wine

Karin Labarai Masu Alaka

Dakarun Zaman Lafiya Na Majalisar Dinkin Duniya Sun Rasa Rayukan Su Afrika
Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe Amurka
Sojin Israela Sunkai Hari Kan Falatsinawa Tsaro
Iran Ta Karyata Tattaunawa Da Washington Afrika
Fargaba Ta Karu Duk Da Tsagaita Wuta Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Amurka Donald Trump Ya Jadda da Kudirinsa Da Kwace Iyakar Greenland Amurka
  • Amurka Zata Fice Daga Iran Cikin Gaggawa Afrika
  • Kasashen Da Suke Kawance Da Amurka Sun Juyawa Trump Baya Afrika
  • An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
  • Dan Hamayya Ya Amince Da Faduwa A Zaben Kasar Benin Afrika
  • Akwai Yiwuwar Shugaban Ƙasar Afirka Ta Tsakiya Touadera Yasamu Nasara A Karo Na Uku Afrika
  • Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya Amurka
  • Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.