Ranar Litinin, Iran ta musanta cewa ta gudanar da shawarwari da Washington, bayan da shugaba Donald Trump ya dakatar da barazanar da yayi na lalata tashoshin wutan lantarki na Iran, sakamakon abunda ya kira tattaunawa mai ma’ana, da wasu jami’an Iran wadanda bai bayyana ko su wanene bane.
Wani jami’i a turai yace kodashike babu wata tattaunawa ido da ido tsakanin kasashen biyu, kasashen Masar, da Pakistan, da wasu kasashen da suke yankin Gulf, suna kai sakonni tsakanin kasashen biyu. Wani jami’i a Pakistan da wata majiya sun gayawa kamfanin dilanciin labarai na Reuters cewa, sai tayiwu a gudanar da shawarwari kai tsaye na kawo karshen yaki tsakanin kasashen biyu cikin wannan mako a Islamabad.
Trump ya wallafa a shafinsa na dandalin sada zumunta da ake kira Truth Social cewa, Amurka da Iran sun gudanar da shawarwari cikakke mai ma’ana, na kawo karshen yakin baki daya a yankin gabas ta tsakiya.
A sakamakon haka ne yace, zai dakatar da barazanar da yayi na kai hari kan cibiyoyin wutan lantarkin Iran, wannan sanarwar ta sa Hannayen jari a kasuwannin duniya suka cira, yayinda farashin mai ya yayi kasa da dala dari akan ko wace gangar danyen mai.
Ahalinda ake ciki kuma, wata jaridar Amurka da ake kira Politico, ta bada labarin cewa Amurka tana auna kakakin Majalisar Dokokin Iran, Mohammed Bagher Ghalibaf a zaman abokin hulda, ko kuma ta goyi bayansa a zaman shugaban kasar nan gaba, kamar yadda jaridar ta fada a jiya Litinin, inda ta ambaci jami’an Amurka biyu dangane da wannan batu.


