Ƙasashen ƙungiyar AES, wato Burkina Faso da Mali da Nijar, sun buɗe gidan talabijin na bai ɗaya domin ƙarfafa zumunci da haɗin kai a tsakaninsu, tare da isar da sahihan labarai ga al’ummomin ƙasashen uku.
Ministocin Harkokin Ƙasashen Waje na ƙasashen AES ne suka rattaba hannu kan yarjejeniyar buɗe gidan talabijin ɗin a ranar 21 ga Disamba, a babban birnin ƙasar Mali, Bamako.
A cewar ministocin, an kafa wannan gidan talabijin ne domin ya zama murya ta bai ɗaya ga ƙasashen, inda zai riƙa bayyana matsayinsu kan muhimman batutuwa da suka shafi siyasa, tsaro, tattalin arziki da ci gaban yankin Sahel.
Sun ƙara da cewa tashar za ta taka muhimmiyar rawa wajen yaƙi da yaɗa labaran ƙarya, da kuma kare al’adu, ɗabi’u da muradun al’ummomin ƙasashen uku.
Haka kuma, sun bayyana cewa gidan talabijin ɗin zai taimaka wajen kusantar da jama’a da gwamnatocinsu, tare da nuna nasarori da ƙalubalen da ƙasashen AES ke fuskanta.
Masu sharhi na ganin cewa buɗe wannan gidan talabijin wata babbar alama ce ta ƙudurin ƙasashen AES na dogaro da kansu a fannin yaɗa labarai da kuma ƙarfafa haɗin kai a yankin Sahel.


